ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Tanzania

Hukumar Zaɓen Tanzania ta bayyana Shugabar ƙasa Samia Suluhu Hassan a matsayin wadda ta lashe zaɓen shugaban ƙasa, duk da cewa zaɓen ya gudana cikin tashin hankali da zubar da jini a sassan ƙasar.

A cewar sakamakon da aka sanar da safiyar Asabar, Suluhu ta samu kusan kashi 98 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa, abin da jam’iyyun adawa suka yi watsi da shi, suna kiran sakamakon “bogi” da “wasan kwaikwayo na dimokuraɗiyya.”

  • An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania
  • Babban Darektan Jaridar The Guardian Ta Tanzaniya: Abubuwan Da Aka Tattauna a Manyan Taruka Biyu Na Sin Na Da Alaka Da Kasashen Duniya

Sai dai jam’iyyar adawa ta Chadema ta ce mutane sama da 700 sun mutu sakamakon tarzomar da ta ɓarke yayin da ake ƙidayar ƙuri’u. Kakakin jam’iyyar, John Kitoka, ya shaida wa kamfanin labarai na AFP cewa mutane fiye da 350 sun mutu a Dar es Salaam, yayin da mutane 200 ke cikin mamata a Mwanza, inda sauran mamatan suka fito daga wasu yankuna na ƙasar.

ADVERTISEMENT

Kitoka ya bayyana cewa adadin zai iya ƙaruwa saboda doka ta hana fita da aka saka tun ranar Laraba, inda ake zargin jami’an tsaro suna ci gaba da kisa da daddare. Sai dai gwamnatin ta Tanzania ta ƙaryata wannan iƙirari, tana mai cewa adadin da aka bayar “ya yi yawa fiye da gaskiya,” tana kuma musanta zargin keta haƙƙin ɗan adam.

Ministan Harkokin Waje, Mahmoud Thabit Kombo, ya ce wasu tsirarun “’yan ta’adda ne suka haddasa matsalar”, yayin da Sakataren MDD, António Guterres, ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa kan zargin amfani da ƙarfin tuwo wajen murƙushe masu zanga-zanga.

LABARAI MASU NASABA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

Shugaba Samia Suluhu Hassan, wadda ke neman wa’adin ta na farko a hukumance bayan ta gaji marigayi John Pombe Magufuli a 2021, ta tsaya takara ƙarƙashin jam’iyyar CCM mai mulki. Sai dai rashin shigar manyan ‘yan adawa da aka hana tsayawa ko aka daure ya jefa shakku kan ingancin zaɓen da aka gudanar, inda masu zanga-zanga suka yi kira da a kafa gwamnatin riƙon ƙwarya da zai shirya sahihin zaɓe a gaba.

Tanzania
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir
  • Abubakar Sulaiman
    Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
  • Abubakar Sulaiman
    ICPC Ta Yi Karar Likitan El-Rufai Kan Ƙirƙirar Jabun Rahoton Lafiya

MASU ALAKA

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.