• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

by Abubakar Sulaiman
1 month ago
Aiyedatiwa

Gwamnan Jihar Ondo, Hon. Lucky Aiyedatiwa, ya samu tarɓa daga ɗumbin magoya baya a dandalin Dimokuraɗiyya (Democracy Park) da ke Akure ranar Juma’a bayan kotun ƙoli ta tabbatar da nasararsa. Gwamnan ya dawo ne daga Abuja inda aka yanke hukuncin da ya tabbatar da sahihancin zaɓensa.

A yayin jawabi ga dubban jama’a, Aiyedatiwa ya gode wa Allah, da mutanen Jihar Ondo da duk masu goyon bayansa a lokacin shari’ar. Ya bayyana kotu a matsayin ginshiƙin dimokuraɗiyya, yana mai jaddada cewa adalci da gaskiya suna da matuƙar muhimmanci wajen ɗorewar mulki. Ya kuma yaba wa lauyoyinsa kan ƙwarewarsu tare da gode wa Shugaba Bola Tinubu bisa jagorancinsa.

  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

“Wannan nasara ba tawa ce kaɗai ba, ta kowa ce a Jihar Ondo,” in ji shi, yana mai ba da tabbacin kyakkyawan shugabanci da isar da alfanun dimokuraɗiyya ga jama’a.Aiyedatiwa

A jawabansu na taya murna, wasu daga cikin manyan baƙi sun bayyana hukuncin kotun a matsayin nasarar jama’a. Hon. Ifedayo Abegunde na hukumar NDDC ya ce hukuncin ya tabbatar da cewa “ƙuri’un jama’a ba a ɓata su ba.” Tsohon mataimakin gwamna, Alhaji Abdulazeez Oluboyo, ya ce Aiyedatiwa ya kafa tarihi da samun nasara a ƙananan hukumomi baki ɗaya, yayin da tsohuwar kwamishina, Mrs. Omowumi Ohwovoriole, ta bayyana hukuncin kotun a matsayin ƙarshen duk wata muhawara kan zaɓen 2024.

Taron ya samu halartar jiga-jigan gwamnati da jam’iyya ciki har da Mataimakin Gwamna, Dr. Olayide Adelami; da Uwargidan Gwamna, Mrs. da Oluwaseun Aiyedatiwa; da Kakakin majalisar jihar, Rt. Hon. Olamide Oladiji; da Sakataren Gwamnati, Dr. Taiwo Fasoranti; da Shugaban Ma’aikata, Prince Segun Omojuwa; da mambobin majalisar zartarwa ta jiha; da manyan jiga-jigan APC; da shugabannin ƙananan hukumomi da na LCDA da sauran fitattun mutane.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

AiyedatiwaAiyedatiwa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Next Post
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.