• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

by Abubakar Sulaiman
6 hours ago
Majalisa

Majalisar Dokoki ta ƙasa (NASS) ta gabatar da sabon shirin da ke neman sauya jadawalin zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnoni na 2027 zuwa watan Nuwamba 2026, maimakon watan Fabrairu ko Maris kamar yadda aka saba.

Wannan mataki yana cikin gyaran dokar zaɓe ta 2022, wanda ya tanadi cewa zaɓe ya gudana kafin kwanaki 185 da ƙarewar wa’adin gwamnati mai ci, wanda ke ƙarewa a ranar 29 ga Mayu. Manufar shirin ita ce a samar da isasshen lokaci don kammala dukkan ƙorafe-ƙorafen dake gaban kotun zaɓe kafin rantsar da sabbin shugabanni.

  • Ko Afirka Za Ta Samu Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya?
  • Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

A yayin taron jin ra’ayoyi da kwamitin haɗin gwuiwa na majalisar dattijai da ta wakilai kan harkokin zaɓe suka gudanar a ranar Litinin, an bayyana cewa sabon tsarin zai taimaka wajen tabbatar da adalci da tsari a harkar zaɓe. Shugaban kwamitin majalisar wakilai, Hon. Adebayo Balogun, ya ce gyaran zai rage lokacin yanke hukunci na kotunan zaɓe daga kwanaki 180 zuwa 90, yayin da kotun ɗaukaka ƙara da kotun ƙoli za su yanke hukunci cikin kwanaki 60 da 35.

Ƙarin gyare-gyaren da aka gabatar sun haɗa da tanadin yin zaɓe da wuri ga wasu rukuni na mutane kamar jami’an tsaro, da ƴan jarida, da ma’aikatan hukumar zaɓe da masu sa ido na cikin gida, a ƙalla kwanaki 14 kafin babban zaɓe. Haka kuma, an ƙarfafa amfani da tsarin aika sakamakon zaɓe ta hanyar lantarki domin tabbatar da gaskiya da inganci, tare da tanadin hukunci ga duk jami’in zaɓe da ya saɓa ƙa’ida ko ya yi sakaci wajen gudanar da aikinsa.

Wakilan hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), ciki har da Farfesa Abdullahi Zuru, sun nuna goyon bayansu ga wannan shirin, suna mai jaddada cewa sauye-sauyen za su inganta tsarin zaɓe, da rage zargin maguɗi, da tabbatar da amincewar ƴan Nijeriya ga sakamakon zaɓe.

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

A cewar su, wannan sabon tsarin zai taimaka wajen gina dimokuraɗiyya mai ƙarfi da ɗorewa a ƙasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba
Ilimi

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
Manyan Labarai

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
nema
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.