• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi Hukumar Shari’a Ta Binciki Sheikh Gadon-Ƙaya Kan Zargin Auren Jinsi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Zargin Luwaɗi Da Maɗigo: Gwamnatin Bauchi Ta Gayyaci Sheikh Gadon-Kaya Don Ƙarin Haske
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta umarci hukumar Shari’ah da ta gaggauta gudanar da bincike kan bidiyon da ke yawo a kafafen sadarwa zumunta inda aka jiyo wani malamin addinin Muslunci da ke Kano, Dakta Abdallah Gadon-Kaya na zargin cewa, akwai wasu da suka taru a jihar Bauchi su na luwaɗi da maɗigo gami da auren jinsi.

 

Ɗan majalisar da ke wakiltar mazaɓar Chinade/Madara, Dakta Nasiru Ahmed Ala, shi ne ya gabatar da ƙudurin neman a gayyato malamin bisa buƙatar gaggawa lura da muhimmanci hakan a yayin zaman majalisar na ranar Talata.

  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu
  • Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Ala, ya bayyana cewa, Malamin addinin, Sheikh Gadon-Kaya, ya shaida wa duniya cewa, masu luwaɗi da maɗigo daga sassan jihohin arewacin Nijeriya, sun haɗu a Bauchi domin sheƙe ayarsu har ma da auren jinsi lamarin da ya ce ya saɓa wa koyarwar addinin musulunci da na Kiristanci.

 

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

A cewar ɗan majalisar, akwai buƙatar hukumar Shari’a ta jihar ta gayyaci Dakta Abdallah Gadon Kaya domin ya zo ya bada hujjojin iƙirarin nasa domin tabbatar da dokokin Shari’a su yi aiki a kan duk wanda aka samu da laifi.

A nasa ɓangaren, Kakakin majalisar dokokin jihar, Abubakar Y. Sulaiman, ya ce, kundin tsarin mulkin ƙasa na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ya bai wa majalisar ƙarfin ikon gayyatar kai tsaye ga wani mutum da ya bayyana a gabanta domin gudanar da wani bincike ko neman ƙarin haske kan kowani bayani da ya shafi ƙasa ko kuma iƙirarin da ya yi.

 

Idan za a tuna dai tun da farko, hukumar Shari’a ta aike da katin gayyata ga Dakta Abdallah Gadon-Kaya domin ya zo ya mata ƙarin haske da cikakken bayani kan iƙirarin nasa da ke zargin wasu da haɗuwa a Bauchi domin yin luwaɗi da maɗigo, amma tun daga wannan lokacin ba a sake jin komai daga wajen hukumar ba.

 

A wani matakin na daban, ƙudurin dokar kafa hukumar HISBA ta jihar Bauchi na 2024 ya tsallake karatu na biyu a gaban majalisar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren JinsiBauchiSheikh Gadon-Kaya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Next Post

Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

2 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

6 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

7 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

8 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

10 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

13 hours ago
Next Post
Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

LABARAI MASU NASABA

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.