• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi Hukumar Shari’a Ta Binciki Sheikh Gadon-Ƙaya Kan Zargin Auren Jinsi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Zargin Luwaɗi Da Maɗigo: Gwamnatin Bauchi Ta Gayyaci Sheikh Gadon-Kaya Don Ƙarin Haske
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta umarci hukumar Shari’ah da ta gaggauta gudanar da bincike kan bidiyon da ke yawo a kafafen sadarwa zumunta inda aka jiyo wani malamin addinin Muslunci da ke Kano, Dakta Abdallah Gadon-Kaya na zargin cewa, akwai wasu da suka taru a jihar Bauchi su na luwaɗi da maɗigo gami da auren jinsi.

 

Ɗan majalisar da ke wakiltar mazaɓar Chinade/Madara, Dakta Nasiru Ahmed Ala, shi ne ya gabatar da ƙudurin neman a gayyato malamin bisa buƙatar gaggawa lura da muhimmanci hakan a yayin zaman majalisar na ranar Talata.

  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu
  • Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Ala, ya bayyana cewa, Malamin addinin, Sheikh Gadon-Kaya, ya shaida wa duniya cewa, masu luwaɗi da maɗigo daga sassan jihohin arewacin Nijeriya, sun haɗu a Bauchi domin sheƙe ayarsu har ma da auren jinsi lamarin da ya ce ya saɓa wa koyarwar addinin musulunci da na Kiristanci.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A cewar ɗan majalisar, akwai buƙatar hukumar Shari’a ta jihar ta gayyaci Dakta Abdallah Gadon Kaya domin ya zo ya bada hujjojin iƙirarin nasa domin tabbatar da dokokin Shari’a su yi aiki a kan duk wanda aka samu da laifi.

A nasa ɓangaren, Kakakin majalisar dokokin jihar, Abubakar Y. Sulaiman, ya ce, kundin tsarin mulkin ƙasa na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ya bai wa majalisar ƙarfin ikon gayyatar kai tsaye ga wani mutum da ya bayyana a gabanta domin gudanar da wani bincike ko neman ƙarin haske kan kowani bayani da ya shafi ƙasa ko kuma iƙirarin da ya yi.

 

Idan za a tuna dai tun da farko, hukumar Shari’a ta aike da katin gayyata ga Dakta Abdallah Gadon-Kaya domin ya zo ya mata ƙarin haske da cikakken bayani kan iƙirarin nasa da ke zargin wasu da haɗuwa a Bauchi domin yin luwaɗi da maɗigo, amma tun daga wannan lokacin ba a sake jin komai daga wajen hukumar ba.

 

A wani matakin na daban, ƙudurin dokar kafa hukumar HISBA ta jihar Bauchi na 2024 ya tsallake karatu na biyu a gaban majalisar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren JinsiBauchiSheikh Gadon-Kaya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Next Post

Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

1 minute ago
Gadon-Kaya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

32 minutes ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

2 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

5 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

8 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

8 hours ago
Next Post
Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Gadon-Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.