ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi Hukumar Shari’a Ta Binciki Sheikh Gadon-Ƙaya Kan Zargin Auren Jinsi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 years ago
Gadon-Kaya

Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta umarci hukumar Shari’ah da ta gaggauta gudanar da bincike kan bidiyon da ke yawo a kafafen sadarwa zumunta inda aka jiyo wani malamin addinin Muslunci da ke Kano, Dakta Abdallah Gadon-Kaya na zargin cewa, akwai wasu da suka taru a jihar Bauchi su na luwaɗi da maɗigo gami da auren jinsi.

 

Ɗan majalisar da ke wakiltar mazaɓar Chinade/Madara, Dakta Nasiru Ahmed Ala, shi ne ya gabatar da ƙudurin neman a gayyato malamin bisa buƙatar gaggawa lura da muhimmanci hakan a yayin zaman majalisar na ranar Talata.

ADVERTISEMENT
  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu
  • Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Ala, ya bayyana cewa, Malamin addinin, Sheikh Gadon-Kaya, ya shaida wa duniya cewa, masu luwaɗi da maɗigo daga sassan jihohin arewacin Nijeriya, sun haɗu a Bauchi domin sheƙe ayarsu har ma da auren jinsi lamarin da ya ce ya saɓa wa koyarwar addinin musulunci da na Kiristanci.

 

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

A cewar ɗan majalisar, akwai buƙatar hukumar Shari’a ta jihar ta gayyaci Dakta Abdallah Gadon Kaya domin ya zo ya bada hujjojin iƙirarin nasa domin tabbatar da dokokin Shari’a su yi aiki a kan duk wanda aka samu da laifi.

A nasa ɓangaren, Kakakin majalisar dokokin jihar, Abubakar Y. Sulaiman, ya ce, kundin tsarin mulkin ƙasa na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ya bai wa majalisar ƙarfin ikon gayyatar kai tsaye ga wani mutum da ya bayyana a gabanta domin gudanar da wani bincike ko neman ƙarin haske kan kowani bayani da ya shafi ƙasa ko kuma iƙirarin da ya yi.

 

Idan za a tuna dai tun da farko, hukumar Shari’a ta aike da katin gayyata ga Dakta Abdallah Gadon-Kaya domin ya zo ya mata ƙarin haske da cikakken bayani kan iƙirarin nasa da ke zargin wasu da haɗuwa a Bauchi domin yin luwaɗi da maɗigo, amma tun daga wannan lokacin ba a sake jin komai daga wajen hukumar ba.

 

A wani matakin na daban, ƙudurin dokar kafa hukumar HISBA ta jihar Bauchi na 2024 ya tsallake karatu na biyu a gaban majalisar.

Gadon-Kaya
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Gadon-Kaya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.