ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi Hukumar Shari’a Ta Binciki Sheikh Gadon-Ƙaya Kan Zargin Auren Jinsi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 years ago
Gadon-Kaya

Majalisar Dokokin Jihar Bauchi ta umarci hukumar Shari’ah da ta gaggauta gudanar da bincike kan bidiyon da ke yawo a kafafen sadarwa zumunta inda aka jiyo wani malamin addinin Muslunci da ke Kano, Dakta Abdallah Gadon-Kaya na zargin cewa, akwai wasu da suka taru a jihar Bauchi su na luwaɗi da maɗigo gami da auren jinsi.

 

Ɗan majalisar da ke wakiltar mazaɓar Chinade/Madara, Dakta Nasiru Ahmed Ala, shi ne ya gabatar da ƙudurin neman a gayyato malamin bisa buƙatar gaggawa lura da muhimmanci hakan a yayin zaman majalisar na ranar Talata.

ADVERTISEMENT
  • An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu
  • Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Ala, ya bayyana cewa, Malamin addinin, Sheikh Gadon-Kaya, ya shaida wa duniya cewa, masu luwaɗi da maɗigo daga sassan jihohin arewacin Nijeriya, sun haɗu a Bauchi domin sheƙe ayarsu har ma da auren jinsi lamarin da ya ce ya saɓa wa koyarwar addinin musulunci da na Kiristanci.

 

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

A cewar ɗan majalisar, akwai buƙatar hukumar Shari’a ta jihar ta gayyaci Dakta Abdallah Gadon Kaya domin ya zo ya bada hujjojin iƙirarin nasa domin tabbatar da dokokin Shari’a su yi aiki a kan duk wanda aka samu da laifi.

A nasa ɓangaren, Kakakin majalisar dokokin jihar, Abubakar Y. Sulaiman, ya ce, kundin tsarin mulkin ƙasa na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ya bai wa majalisar ƙarfin ikon gayyatar kai tsaye ga wani mutum da ya bayyana a gabanta domin gudanar da wani bincike ko neman ƙarin haske kan kowani bayani da ya shafi ƙasa ko kuma iƙirarin da ya yi.

 

Idan za a tuna dai tun da farko, hukumar Shari’a ta aike da katin gayyata ga Dakta Abdallah Gadon-Kaya domin ya zo ya mata ƙarin haske da cikakken bayani kan iƙirarin nasa da ke zargin wasu da haɗuwa a Bauchi domin yin luwaɗi da maɗigo, amma tun daga wannan lokacin ba a sake jin komai daga wajen hukumar ba.

 

A wani matakin na daban, ƙudurin dokar kafa hukumar HISBA ta jihar Bauchi na 2024 ya tsallake karatu na biyu a gaban majalisar.

Gadon-Kaya
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
Gadon-Kaya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

MASU ALAKA

Gadon-Kaya
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gadon-Kaya
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

Wakilai 408 Daga Kasashen Afirka 48 Sun Yi Rajistar Halartar Taron ’Yan Kasuwa Karo Na 8

LABARAI MASU NASABA

Gadon-Kaya

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gadon-Kaya

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.