• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakalar Naira Tiriliyan 2 A Ma’aikatun Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilai ta umarci kwamitinta kan samar da abinci mai gina jiki da wadatar abinci, fitar da amfanin gona da ayyuka, da kwalejojin aikin gona da na cibiyoyi da na kudi da su gudanar da cikakken bincike kan zargin rashin amfani ko kin aiwatar da shirye-shiryen gwamnati da kudaden bangaren noma daga sashi-sashi, hukumomi da shirye-shiryen da manufofin gwamnatin tarayya a wajen ma’aikatar harkokin gona da wadata kasa da abinci.

Wannan na zuwa ne bayan kudirin da Hon. Chike Okafor ya gabatar a yayin zaman majalisar a Abuja.
Ofafor ya lura kan cewa akwai karancin abinci da kuma cutar tamowa a Nijeriya, tare da zargin karkatar da kudaden da aka ware domin aiwatar da shirye-shiryen da manufofin gona da niyyar bunkasa harkokin noma da kayan abinci a Nijeriya.

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja
  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

Ya lura kan cewa gwamnatin tarayya ta yi shirye-shirye da tsare-tsare daban-daban cikin shekaru takwas da suka wuce ta kashe makuden kudade sama da tiriliyan biyu wajen daukan nauyin shirye-shiryen manufofin noma da manufar wadata kasar da abinci, sai dai kuma zargin karkatar da kudaden da rashin aiwatar da shirye-shiryen na kara fitowa fili ta yadda Nijeriya ke ci gaba da fuskantar karancin abinci da rashin abinci mai gina jiki.

A cewarsa, rahotonni da kuma zarge-zargen tafka rashawa, karkatar da kudade, da tafka kura-kurai su ne suka mamaye shirye-shiryen gwamnatin ta yadda kudaden da aka ware ba su yi amfanin da aka yi hankoro ba, inda a cewarsa, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba da tallafi ga manoma na ‘Anchor Borrowers’ ya rabar da sama da naira tiriliyan I.12 ga manoma miliyan 4.67.

“Shirin NIRSAL ya rabar da sama da naira biliyan dari biyu da sha biyar da miliyan sittin da shiya zuwa yanzu domin saukaka ayyukan gona da kasuwancin noma.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

“Bankin masana’antu (BOI) ya fitar da sama da naira biliyan uku ga kananan manoma dubu 22 ta hannun shirin ABCF. Kari kan rancen biliyan 59.4 ga ‘yan kasuwan da ke harkar noma.

“A 2023, gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin rancen naira biliyan 5 ta bankin manoma (BOA) makiyaya a fadin kasar nan. A watan Maris na 2024 asusun tallafin harkokin noma na kasa (NADF) ya kaddamar da dawo da shirin biliyan 1.6 domin dakile cuta a ginger da wasu shirye-shirye.”

Ya ce, bayan wadannan akwai shirye-shirye da dama dukka da gwamnati ta samar da nufin shawo kan karancin abinci da wadata kasa da abinci da abinci mai gina jiki, amma abun takaici har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar karancin abin da za su ci da wanda zai gina musu jiki. Don haka ne ya ce akwai bukatar kaddamar da bincike domin gano yadda aka kashe wadannan kudaden ko kuma inda suka makale.

Domin tabbatar da gaskiya da adalci, majalisar ta amince da kudirin tare da tsammanin cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin mako hudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaEFCCICPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Jinping Ya Ba Da Umarni Kan Aikin Tinkarar Ambaliyar Ruwa A Kasar Sin

Next Post

Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

50 minutes ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

9 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

11 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

13 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

14 hours ago
Next Post
Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.