ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakalar Naira Tiriliyan 2 A Ma’aikatun Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
majalisar kasa

Majalisar wakilai ta umarci kwamitinta kan samar da abinci mai gina jiki da wadatar abinci, fitar da amfanin gona da ayyuka, da kwalejojin aikin gona da na cibiyoyi da na kudi da su gudanar da cikakken bincike kan zargin rashin amfani ko kin aiwatar da shirye-shiryen gwamnati da kudaden bangaren noma daga sashi-sashi, hukumomi da shirye-shiryen da manufofin gwamnatin tarayya a wajen ma’aikatar harkokin gona da wadata kasa da abinci.

Wannan na zuwa ne bayan kudirin da Hon. Chike Okafor ya gabatar a yayin zaman majalisar a Abuja.
Ofafor ya lura kan cewa akwai karancin abinci da kuma cutar tamowa a Nijeriya, tare da zargin karkatar da kudaden da aka ware domin aiwatar da shirye-shiryen da manufofin gona da niyyar bunkasa harkokin noma da kayan abinci a Nijeriya.

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja
  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

Ya lura kan cewa gwamnatin tarayya ta yi shirye-shirye da tsare-tsare daban-daban cikin shekaru takwas da suka wuce ta kashe makuden kudade sama da tiriliyan biyu wajen daukan nauyin shirye-shiryen manufofin noma da manufar wadata kasar da abinci, sai dai kuma zargin karkatar da kudaden da rashin aiwatar da shirye-shiryen na kara fitowa fili ta yadda Nijeriya ke ci gaba da fuskantar karancin abinci da rashin abinci mai gina jiki.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, rahotonni da kuma zarge-zargen tafka rashawa, karkatar da kudade, da tafka kura-kurai su ne suka mamaye shirye-shiryen gwamnatin ta yadda kudaden da aka ware ba su yi amfanin da aka yi hankoro ba, inda a cewarsa, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba da tallafi ga manoma na ‘Anchor Borrowers’ ya rabar da sama da naira tiriliyan I.12 ga manoma miliyan 4.67.

“Shirin NIRSAL ya rabar da sama da naira biliyan dari biyu da sha biyar da miliyan sittin da shiya zuwa yanzu domin saukaka ayyukan gona da kasuwancin noma.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Bankin masana’antu (BOI) ya fitar da sama da naira biliyan uku ga kananan manoma dubu 22 ta hannun shirin ABCF. Kari kan rancen biliyan 59.4 ga ‘yan kasuwan da ke harkar noma.

“A 2023, gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin rancen naira biliyan 5 ta bankin manoma (BOA) makiyaya a fadin kasar nan. A watan Maris na 2024 asusun tallafin harkokin noma na kasa (NADF) ya kaddamar da dawo da shirin biliyan 1.6 domin dakile cuta a ginger da wasu shirye-shirye.”

Ya ce, bayan wadannan akwai shirye-shirye da dama dukka da gwamnati ta samar da nufin shawo kan karancin abinci da wadata kasa da abinci da abinci mai gina jiki, amma abun takaici har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar karancin abin da za su ci da wanda zai gina musu jiki. Don haka ne ya ce akwai bukatar kaddamar da bincike domin gano yadda aka kashe wadannan kudaden ko kuma inda suka makale.

Domin tabbatar da gaskiya da adalci, majalisar ta amince da kudirin tare da tsammanin cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin mako hudu.

majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
majalisa
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.