• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakalar Naira Tiriliyan 2 A Ma’aikatun Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
12 months ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilai ta umarci kwamitinta kan samar da abinci mai gina jiki da wadatar abinci, fitar da amfanin gona da ayyuka, da kwalejojin aikin gona da na cibiyoyi da na kudi da su gudanar da cikakken bincike kan zargin rashin amfani ko kin aiwatar da shirye-shiryen gwamnati da kudaden bangaren noma daga sashi-sashi, hukumomi da shirye-shiryen da manufofin gwamnatin tarayya a wajen ma’aikatar harkokin gona da wadata kasa da abinci.

Wannan na zuwa ne bayan kudirin da Hon. Chike Okafor ya gabatar a yayin zaman majalisar a Abuja.
Ofafor ya lura kan cewa akwai karancin abinci da kuma cutar tamowa a Nijeriya, tare da zargin karkatar da kudaden da aka ware domin aiwatar da shirye-shiryen da manufofin gona da niyyar bunkasa harkokin noma da kayan abinci a Nijeriya.

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja
  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

Ya lura kan cewa gwamnatin tarayya ta yi shirye-shirye da tsare-tsare daban-daban cikin shekaru takwas da suka wuce ta kashe makuden kudade sama da tiriliyan biyu wajen daukan nauyin shirye-shiryen manufofin noma da manufar wadata kasar da abinci, sai dai kuma zargin karkatar da kudaden da rashin aiwatar da shirye-shiryen na kara fitowa fili ta yadda Nijeriya ke ci gaba da fuskantar karancin abinci da rashin abinci mai gina jiki.

A cewarsa, rahotonni da kuma zarge-zargen tafka rashawa, karkatar da kudade, da tafka kura-kurai su ne suka mamaye shirye-shiryen gwamnatin ta yadda kudaden da aka ware ba su yi amfanin da aka yi hankoro ba, inda a cewarsa, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba da tallafi ga manoma na ‘Anchor Borrowers’ ya rabar da sama da naira tiriliyan I.12 ga manoma miliyan 4.67.

“Shirin NIRSAL ya rabar da sama da naira biliyan dari biyu da sha biyar da miliyan sittin da shiya zuwa yanzu domin saukaka ayyukan gona da kasuwancin noma.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

“Bankin masana’antu (BOI) ya fitar da sama da naira biliyan uku ga kananan manoma dubu 22 ta hannun shirin ABCF. Kari kan rancen biliyan 59.4 ga ‘yan kasuwan da ke harkar noma.

“A 2023, gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin rancen naira biliyan 5 ta bankin manoma (BOA) makiyaya a fadin kasar nan. A watan Maris na 2024 asusun tallafin harkokin noma na kasa (NADF) ya kaddamar da dawo da shirin biliyan 1.6 domin dakile cuta a ginger da wasu shirye-shirye.”

Ya ce, bayan wadannan akwai shirye-shirye da dama dukka da gwamnati ta samar da nufin shawo kan karancin abinci da wadata kasa da abinci da abinci mai gina jiki, amma abun takaici har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar karancin abin da za su ci da wanda zai gina musu jiki. Don haka ne ya ce akwai bukatar kaddamar da bincike domin gano yadda aka kashe wadannan kudaden ko kuma inda suka makale.

Domin tabbatar da gaskiya da adalci, majalisar ta amince da kudirin tare da tsammanin cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin mako hudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaEFCCICPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Jinping Ya Ba Da Umarni Kan Aikin Tinkarar Ambaliyar Ruwa A Kasar Sin

Next Post

Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

3 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

5 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

7 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

12 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

13 hours ago
Next Post
Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.