• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Binciki Zargin Badakalar Naira Tiriliyan 2 A Ma’aikatun Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
majalisar kasa

Majalisar wakilai ta umarci kwamitinta kan samar da abinci mai gina jiki da wadatar abinci, fitar da amfanin gona da ayyuka, da kwalejojin aikin gona da na cibiyoyi da na kudi da su gudanar da cikakken bincike kan zargin rashin amfani ko kin aiwatar da shirye-shiryen gwamnati da kudaden bangaren noma daga sashi-sashi, hukumomi da shirye-shiryen da manufofin gwamnatin tarayya a wajen ma’aikatar harkokin gona da wadata kasa da abinci.

Wannan na zuwa ne bayan kudirin da Hon. Chike Okafor ya gabatar a yayin zaman majalisar a Abuja.
Ofafor ya lura kan cewa akwai karancin abinci da kuma cutar tamowa a Nijeriya, tare da zargin karkatar da kudaden da aka ware domin aiwatar da shirye-shiryen da manufofin gona da niyyar bunkasa harkokin noma da kayan abinci a Nijeriya.

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Minista Da Sanatar Abuja
  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma

Ya lura kan cewa gwamnatin tarayya ta yi shirye-shirye da tsare-tsare daban-daban cikin shekaru takwas da suka wuce ta kashe makuden kudade sama da tiriliyan biyu wajen daukan nauyin shirye-shiryen manufofin noma da manufar wadata kasar da abinci, sai dai kuma zargin karkatar da kudaden da rashin aiwatar da shirye-shiryen na kara fitowa fili ta yadda Nijeriya ke ci gaba da fuskantar karancin abinci da rashin abinci mai gina jiki.

A cewarsa, rahotonni da kuma zarge-zargen tafka rashawa, karkatar da kudade, da tafka kura-kurai su ne suka mamaye shirye-shiryen gwamnatin ta yadda kudaden da aka ware ba su yi amfanin da aka yi hankoro ba, inda a cewarsa, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ba da tallafi ga manoma na ‘Anchor Borrowers’ ya rabar da sama da naira tiriliyan I.12 ga manoma miliyan 4.67.

“Shirin NIRSAL ya rabar da sama da naira biliyan dari biyu da sha biyar da miliyan sittin da shiya zuwa yanzu domin saukaka ayyukan gona da kasuwancin noma.

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

“Bankin masana’antu (BOI) ya fitar da sama da naira biliyan uku ga kananan manoma dubu 22 ta hannun shirin ABCF. Kari kan rancen biliyan 59.4 ga ‘yan kasuwan da ke harkar noma.

“A 2023, gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirin rancen naira biliyan 5 ta bankin manoma (BOA) makiyaya a fadin kasar nan. A watan Maris na 2024 asusun tallafin harkokin noma na kasa (NADF) ya kaddamar da dawo da shirin biliyan 1.6 domin dakile cuta a ginger da wasu shirye-shirye.”

Ya ce, bayan wadannan akwai shirye-shirye da dama dukka da gwamnati ta samar da nufin shawo kan karancin abinci da wadata kasa da abinci da abinci mai gina jiki, amma abun takaici har yanzu ‘yan Nijeriya na fama da matsalar karancin abin da za su ci da wanda zai gina musu jiki. Don haka ne ya ce akwai bukatar kaddamar da bincike domin gano yadda aka kashe wadannan kudaden ko kuma inda suka makale.

Domin tabbatar da gaskiya da adalci, majalisar ta amince da kudirin tare da tsammanin cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin mako hudu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Next Post
Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

Shugabar Peru: Ajandar Duniya Da Shugaba Xi Ya Gabatar Na Da Matukar Muhimmanci Ga Zaman Lafiyar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.