Kwamitin Majalisar Dattawa na sake duba kundin tsarin mulki na 1999 yana nazarin shawarwari 31 na ƙirƙirar sabbin jihohi, gami da buƙatun Arewa maso gabas (7), Arewa maso yamma (6), da kudu maso gabas (3).
Bayanai sun nuna cewa majalisar ta kuma yi niyyar ba wa ƙananan hukumomi 774 cikakken ‘yancin kai, yayin da za ta yi nazarin kundin dokoki 20 na gyaran shari’a da kafa wa’adin yanke hukunci.
- Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
- EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Wannan ya zo ne daidai lokacin da majalisar ta shirya taron jin ra’ayin jama’a na kwana biyu a shiyyoyi shida na ƙasar don tattara ra’ayoyin mutane kan gyare-gyaren kundin tsarin mulki.
Kwamitin, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibrin, zai yi nazarin muhimman batutuwa kamar:
1. Ƴancin ƙananan hukumomi
2. Gyaran zaɓe da shari’o’in zaɓe
3. Ƙirƙirar sabbin jihohi
4. Samar da Ƴansandan jihohi
5. Haɗa kai don gudanar da mulki
Daga cikin muhimman shawarwari, akwai na kafa hukumar zaɓen ƙananan hukumomi (NALGEC), ƙara kujeru ga mata a majalisu, da ba wa ‘yan Nijeriya dake ƙasashen waje damar yin zaɓe.
Hakanan, akwai shawarwarin sauya wasu abubuwa daga jerin abubuwan da majalisar tarayya ke da ikon yi zuwa na majalisun jihohi, da kuma ƙirƙirar Majalisar Sarakuna ta ƙasa.
Kwamitin ya yi kira ga duk ‘yan ƙasa da su halarci tarurrukan sauraron ra’ayin jama’a da za a gudanar a:
– Lagos (Kudu maso Yamma)
– Enugu (Kudu maso Gabas)
– Ikot Ekpene (Kudu maso Kudu)
– Jos (Arewa Tsakiya)
– Maiduguri (Arewa maso Gabas)
– Kano (Arewa maso Yamma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp