• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Dokar Dawo Da Tsohon Taken Kasa

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta amince da dokar dawo da tsohon taken kasar nan, a wani yunkuri na dabbaka kishi a zukatan ‘yan Nijeriya.

Sai dai wasu ‘yan majalisar sun nuna takaicinsu kan wannan mataki da majalisar ta dauka.

  • An Kashe Mutane 5000, An Sace 7000 Cikin Shekara 1 A Mulkin Tinubu – Bincike
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Ingantattu Kuma Wadatattun Guraben Ayyukan Yi

Wannan doka ce da ‘yan majalisar suka ba ta muhimmanci da kuma hanzarta amincewa da ita a cikin kwanaki biyu kacal,

Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa, Okpeyemi Bamidele ne, ya dauki nauyin dokar dawo da tsohon taken Nijeriya, wanda ‘yan majalisar ke ganin harufan da aka yi amfani da su a cikin taken suna da ma’ana sosai kuma zai karfafa gwiwar al’ummar kasar nan wajen kaunar juna da hadin kai da kuma kyautata zamantakewa.

Sanata Rufa’i Hanga yana cikin masu wannan tunanin da ya ce tsohon taken Nijeriya waka ce da za ta kara karfafa kishin kasa a tsakanin ‘yan Nijeriya wadanda suka rayu cikin wannan zamanin, kuma sun fahimci muhimmiyar rawar da ta taka a tarihin al’ummarmu.

Labarai Masu Nasaba

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Hanga, ya ce taken Nijeriya da ake amfani da shi yanzu sojoji ne suka kawo shi kuma bai yi ma’ana kaman tsohon ba shi ya sa majalisa ta yi gaggawar amincewa da dokar saboda yaran wannan zamani su yi koyi da kalmomin taken domin ya sauya musu tunani.

Sai dai dan majalisar wakilai, Mohammed Shehu Fagge ya yi suka ne kan matakin da aka dauka na dawo da tsohon taken, inda ya yi tsokaci cewa, kawo wannan magana na sauya taken rashin sanin ciwon kai ne.

Shehu, ya ce a wannan hali da ‘yan kasa ke ciki na yunwa, fatara da rashi da sauran abubuwa makamantansu su ya fi dacewa a mayar da hankali a kai.

Shehu, ya ce shugabanin majalisa ba su yi tunani ba, domin ba shi ne abin da ‘yan kasa ke so ba.

Ya ce kamata ya yi a kalli dokoki da za su amfana wa talakan kasa da abubuwa da za su kawo wa rayuwarsu sauyi.

Shehu ya ce har yanzu majalisa ba ta kammala aiki kan kasafin kudin 2024 ba, saboda haka yana kira da a fuskanci bukatun al’umma.

Sai dai Sanata Mustapha Habib daga mazabar Jigawa ta Kudu, ya yaba da matakin da majalisa ta dauka, inda ya ce yana goyon bayan sauya taken, domin wakar da shi ya sani kenan tun yana yaro.

Habib ya ce taken yana da ma’ana kuma zai koyar da kishin kasa da kaunar juna.

Wannan tsohon taken Nijeriya dai wata baturiya mai suna Lillian Jean Williams ce, ta rubuta shi a lokacin da Nijeriya ta samu ‘yancin kai a 1960.

An daina amfani da taken ne a1978 bayan da aka samo wani sabon taken da wani dan Nijeriya mai suna Ben Odiase ya rubuta.

Dokar dawo da taken dai na jiran sa hannun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Majalisar DattawaTaken Kasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Mutane 5000, An Sace 7000 Cikin Shekara 1 A Mulkin Tinubu – Bincike

Next Post

CJN Ya Yi Sammacin Babban Alkalin Kano Da Alkalin Tarayya Kan Saba Umarnin Kotu

Related

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

25 minutes ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

4 hours ago
An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

5 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

6 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

9 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

24 hours ago
Next Post
CJN Ya Yi Sammacin Babban Alkalin Kano Da Alkalin Tarayya Kan Saba Umarnin Kotu

CJN Ya Yi Sammacin Babban Alkalin Kano Da Alkalin Tarayya Kan Saba Umarnin Kotu

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya HaÉ—in Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon SharaÉ—i Na BuÉ—e Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon SharaÉ—i Na BuÉ—e Asusun Banki

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.