ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Dokar Dawo Da Tsohon Taken Kasa

by Sadiq
2 years ago
Majalisar

Majalisar Dattawa ta amince da dokar dawo da tsohon taken kasar nan, a wani yunkuri na dabbaka kishi a zukatan ‘yan Nijeriya.

Sai dai wasu ‘yan majalisar sun nuna takaicinsu kan wannan mataki da majalisar ta dauka.

  • An Kashe Mutane 5000, An Sace 7000 Cikin Shekara 1 A Mulkin Tinubu – Bincike
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Samar Da Ingantattu Kuma Wadatattun Guraben Ayyukan Yi

Wannan doka ce da ‘yan majalisar suka ba ta muhimmanci da kuma hanzarta amincewa da ita a cikin kwanaki biyu kacal,

ADVERTISEMENT

Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa, Okpeyemi Bamidele ne, ya dauki nauyin dokar dawo da tsohon taken Nijeriya, wanda ‘yan majalisar ke ganin harufan da aka yi amfani da su a cikin taken suna da ma’ana sosai kuma zai karfafa gwiwar al’ummar kasar nan wajen kaunar juna da hadin kai da kuma kyautata zamantakewa.

Sanata Rufa’i Hanga yana cikin masu wannan tunanin da ya ce tsohon taken Nijeriya waka ce da za ta kara karfafa kishin kasa a tsakanin ‘yan Nijeriya wadanda suka rayu cikin wannan zamanin, kuma sun fahimci muhimmiyar rawar da ta taka a tarihin al’ummarmu.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Hanga, ya ce taken Nijeriya da ake amfani da shi yanzu sojoji ne suka kawo shi kuma bai yi ma’ana kaman tsohon ba shi ya sa majalisa ta yi gaggawar amincewa da dokar saboda yaran wannan zamani su yi koyi da kalmomin taken domin ya sauya musu tunani.

Sai dai dan majalisar wakilai, Mohammed Shehu Fagge ya yi suka ne kan matakin da aka dauka na dawo da tsohon taken, inda ya yi tsokaci cewa, kawo wannan magana na sauya taken rashin sanin ciwon kai ne.

Shehu, ya ce a wannan hali da ‘yan kasa ke ciki na yunwa, fatara da rashi da sauran abubuwa makamantansu su ya fi dacewa a mayar da hankali a kai.

Shehu, ya ce shugabanin majalisa ba su yi tunani ba, domin ba shi ne abin da ‘yan kasa ke so ba.

Ya ce kamata ya yi a kalli dokoki da za su amfana wa talakan kasa da abubuwa da za su kawo wa rayuwarsu sauyi.

Shehu ya ce har yanzu majalisa ba ta kammala aiki kan kasafin kudin 2024 ba, saboda haka yana kira da a fuskanci bukatun al’umma.

Sai dai Sanata Mustapha Habib daga mazabar Jigawa ta Kudu, ya yaba da matakin da majalisa ta dauka, inda ya ce yana goyon bayan sauya taken, domin wakar da shi ya sani kenan tun yana yaro.

Habib ya ce taken yana da ma’ana kuma zai koyar da kishin kasa da kaunar juna.

Wannan tsohon taken Nijeriya dai wata baturiya mai suna Lillian Jean Williams ce, ta rubuta shi a lokacin da Nijeriya ta samu ‘yancin kai a 1960.

An daina amfani da taken ne a1978 bayan da aka samo wani sabon taken da wani dan Nijeriya mai suna Ben Odiase ya rubuta.

Dokar dawo da taken dai na jiran sa hannun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
CJN Ya Yi Sammacin Babban Alkalin Kano Da Alkalin Tarayya Kan Saba Umarnin Kotu

CJN Ya Yi Sammacin Babban Alkalin Kano Da Alkalin Tarayya Kan Saba Umarnin Kotu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.