A yammacin ranar Laraba ne Majalisar Dattawa ta tabbatar da tantance sunayen ministoci bakwai da shugaban kasa Bola Tinubu ya mika mata domin nada su a matsayin ministoci da mambobin majalisar zartarwa ta tarayya (FEC).
Kudurin Majalisar ya biyo bayan tantance sunayen ministocin da Sanatocin suka yi na tsawon sa’o’i.
- Tattalin Arziƙi: Jega Ya Gargaɗi Nijeriya Kan Amincewa Da Shawarwarin IMF Da Bankin Duniya
- Mene Ne Burin Amurka Wajen Sake Yada Jita-Jitar “Barazanar ‘Yan Leken Asirin Kasar Sin”
Ministocin da aka nada sun hada da Dr. Nentawe Yilwatda, ministar harkokin jin kai da rage talauci; Muhammadu Maigari Dingyadi, Ministan Kwadago da Aiki, da Amb. Bianca Odinaka Odumegu-Ojukwu, Karamar Ministan Harkokin Waje.
Sauran sun hada da Dr. Jumoke Oduwole, Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Idi Muktar Maiha, Ministan kula da kiwon Dabbobi; Rt. Hon. Yusuf Abdullahi Ata, Karamin Ministan Gidaje, da Dr. Suwaiba Said Ahmad, Karamar Ministan Ilimi.
In ba a manta ba, a cikin wata wasika da shugaba Tinubu ya aikewa majalisar dattawa a makon da ya gabata ya bukaci majalisar ta gaggauta tantance ministocin domin fara aikin lalubo mafita ga halin da kasar ke ciki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp