• English
  • Business News
Tuesday, September 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha

by Naziru Adam Ibrahim
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta buɗe ofishin Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, wanda hakan ke nuna alamar ƙarshen taƙaddamar da ta daɗe tana yi da Shugaban Majalisar Dattawan Godswill Akpabio.

A yau Talata 23 ga watan Satumban 2025, ne jami’in tsaron majalisar, tare da haɗin gwuiwar dakarun tsaro, suka sake buɗe ofishin Sanata Natasha, mai lamba 205 a harabar Majalisar Dattawa.

  • Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas
  • Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Wannan mataki ya dawo mata da cikakken damar shiga harabar majalisar da ofishinta, wanda hakan zai iya bai wa Sanatar damar komawa zaman Majalisar Dattawa lokacin da ‘yan majalisa za su koma bakin aiki a ranar 7 ga watan Oktoban 2025.

Majiyoyi sun ce an ɗauki wannan mataki ne a wani taron shugabancin majalisar da aka yi a ranar Litinin, inda aka tsara cewa shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Abba Moro, zai gabatar da ƙudiri don a yi uzuri tare da mara masa baya, sai a gabatar da shi a gaban majalisar inda za ta bayar da haƙuri.

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, wadda ta taɓa shugabantar Kwamitin Majalisar Dattawa kan harkokin tafiye-tafiyen ƙasashen waje da Ƙungiyoyi Masu Zaman Kansu, an dakatar da ita na tsawon watanni shida a watan Maris, bayan ta nuna adawa da sauya mata kujera wanda majalisar ta zarge ta da saɓa dokokinta.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

Yanzu da aka buɗe ofishinta kafin komawar zaman majalisar, hankali ya karkata kan zaman majalisar na watan Oktoba, don ganin ko za a gabatar da kuɗirin dawowarta, da kuma ko za a tilasta mata ta nemi afuwa kafin ta dawo ta zauna a kujerarta a cikin zauren majalisar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DakatarwaMajalisar DattawaOfishiSanata Natasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

Next Post

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

Related

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

2 hours ago
Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

4 hours ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

5 hours ago
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
Manyan Labarai

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

9 hours ago
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
Manyan Labarai

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

18 hours ago
BUK
Manyan Labarai

Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau

23 hours ago
Next Post
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

September 23, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha

September 23, 2025
Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

September 23, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

September 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

September 23, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

September 23, 2025
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

September 23, 2025
He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

September 22, 2025
Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

September 22, 2025
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

September 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.