ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

by Leadership Hausa
8 months ago
Amurka

Bisa lamarin da ya ya shafi lamuran kasa da kasa, musamman idan aka samu wata matsala da ta shafi huddar jakandanci, a kan yi kokari ne, domin lalubo da mafita.

Amma, irin daukar irin wannan matakin, batun bahaka ya ke ga shugaban Amurka ba, duba da yadda Donald Trump ba, duba da yadda a ranar Asabar da ta gabata, ya yi kurarin barazanar aukawa Nijeriya da yaki da makamai.

  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

Trump, ya yi wannan barazanar ce kan cewar, ana yiwa mabiya addiin Kirista kisan gilla a kasar nan, wanda hakan ya sanya, ya umarci sahsne yaki na Amurka, wato Pentagon, da ya fara shirya makamai, domin kawo wa Nijeriya yaki, wanda a na sa ganin ikirarin na sa na kisan gillar, tauye hakkin ‘yan Adama ne.

ADVERTISEMENT

Kazalika, Trump ya alakanta kasar, a matsayin cikin jeren kasa ta musamman da bata bayar da ‘yancin gudanar da yin addini, wanda kuma alhali, ba shi da wasu kwararan hujjoji kan wannan ikirarin na sa.

Wannan batun, na barazanar Trump, ta samo asali ne ga furucin matsalar tsaro a kasar nan, da wani sanata na majalisar Amurka Ted Cruz, ya jiero da ita.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Sai dai, bisa batun gasakiya, karya ce tsagwaronta kan batun kisan kiyashin da ake yamadidin cewa, ana yiwa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya.

Bugu da kari, wannan batun ana wani yunkuri ne na son kawo rudadi a kasar nna, musamman duba da cewa, masu son kawo rudadin, a zahiri, sun jahilci irin yanayin sarkakiyar lamarin tsaro na kasar nan.

Wannan Jaridar, ta sha yin tsokaci, kan kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar nan, tare da kuma yawan gabatar da kira ga Gwamnatin kasar da ta tashi tsaye, domin daukar matakan da suka dace, na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

Batun aikata ta’addanci, yin garkuwa da mutane da kuma aukuwar rikici a tsakanin manoma da makiyaya, matsaloli ne, da ke shafar kowannen dan Nijeriya, wanda kuma Trump da masu ba shi shawara, suka jahilci hakan, musammman duba da cewa, akasarin wadannan matsalalin, na aukuwa Musulmi da Kirista ne.

Wani abin duba wa a nan shi ne, akasarin hare-haren ‘yan ta’addara Boko Hrama na kai wa kan Musulmi da ke Arewacin Nijeriya, wanda Trump, ya kafa hujar da cewa, ana kashe Kiristoci ne, inda kuma hare-haren, suka nuna cewa, anfi hallaka Musulmai, fiye da Kiristoci.

Ayyana matsalar tsaron kasar da Trump ya yin a yi wa Kiristoci kisan kare dangi wani abu ne, da yake da matukar hadari.

Martanin da shugaba Bola Tinubu ya mayarwa da Trump kan wannan ikirarin na sa, abu ne da ya dace, musamman cewar da ya yi a Nijeriya ana bai wa kowanne dan kasar, ‘yancin yin addininsa, ba tare da wata tsangwama ba, musamman kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar, ya tanadar.

Bugu da kari, idan har Trump na nuna damuwa kan ikirarinsa na ana yi wa Kiristocin kasar kisan gilla, to su kuma Kiristocin da aka hallak a zirin Gaza biyo bayan hare-haren kasar Isra’ila fa?

Kuma mai ya sa ba zai yi amfani da karfin ikon gwamnatinsa na dakatar da yakar kasar Ukraine, da kasar Rasha ke ci gaba da yi ba, duba da yadda aka kashe dubban Kiristoci a kasar?

Amsar a nan ita ce, Trump ba wai na da nufi bai wa Kiristocin kasar nan kariya bane, wani bakar manufa ce kawai da yake son cimma burinsa.

Tarihi ba zai sanya mu yi saurin manta wa da mamayar da Amurka ta yiwa kasar Afghanistan a 2001 ba don kifar da gwamnatin Taliban wadda ta alakantan, a matsayin ‘yan ta’adda.

A lokacin mamayar, sama da mutane 200,000 ne, suka rasa rayukansu, amma duk da hakan, Taliban ta sake dawo wadda a yanzu, ta ke ci gaba da jan ragamar shugabancin kasar.

Kazalika, Amurka ta mamaye kasar Iraki a 2003, ta cere shugaban sojin kasar kasa marigayi Saddam Hussein, inda sama da mutane 150,000 suka rasa rayukansu sabo da hare-haren Amurka.

Hakazalika, ta kai wata mamayar a kasar Lbiyia ta cere marigayi Gaddafi, wanda har yanzu, kasar ba ta saitu ba, inda kuma burbushin yakin na Lbiya ya haifar da shigar makamai cikin kasar nan da ‘yan Boko Haram da ‘yan bindiga daji da kuma wasu Fulani ke yin amfani da su, wajen kai hare-hare a Nijeriya.

Yin amfani da karin soji da Amurka ta yi barazanar yi kan Nijeriya ba sanya matsalar tsaron kasar nan, ta kau ba, sai dai ma, kara tabarbarar da tsaron kasar.

Idan har da gaske Amurka ta ke yi na taimaka wa Nijeriya ta magance kalubalen rashin tsaronta ba ta hanyar barazana ya kamata ta bullowa kasar ba, kamata ya yi ta taimaka wa Nijeriya da kudade da makamai domin kawo karshen matsalar da kuma yin musayar bayanan sirri.

Amma yi wa Nijeriya wannan barazar, tamkar wani cin fuska ne.

A zahiri barazanar ta Trump, ba wai yana nufin bai wa Kiristocin Nijeriya kariya bane, amma wani salon na ne kawai na son nuna karfin iko da kuma son kawo rabuwar kanuwanan ‘yan Nijeriya.

Ya kamata Trump ya mayar da hankali kan matsalolin da ke ci gaba da addabar kasarsa ne, ba wai yin shiga sharo ba shanu, kan batun da ya shafi Nijeriya ba.

Sai dai, a nan za mu iya cewa, wannan barazar ta sa, dole ne ta zama wata ankawarar ga masu rike da madafun iko a kasar nan, wajen lalubo da mafita kan matsalar tsaro da kasar da kasar ke ci gaba da fuskanta.

Amurka
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.