• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Binciken Badakalar Mai

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Binciken Badakalar Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da jama’a ke nuna bacin rai da rashin gamsuwa sakamakon karin farashin man fetur da kuma karancinsa a kasuwanni, majalisar dattawa ta dakatar da binciken lamarin wanda ya haifar da rudani.

Jagoran majalisar dattawa kuma shugaban kwamitin binciken badakala a bangaren masana’antar man fetur ta Nijeriya, Sanata Opeyemi Bamidele ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a farkon makon nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kaduna: Ruftawar Hanya Sakamakon Ambaliyar Ruwa Ta Katse Garuruwa Biyar A Lere 

A cikin sanarwar da Bamidele ya fitar bai yi bayanin dalilin dage binciken ba, amma ya yi ikirarin cewa an dauki matakin ne domin amfanar da kasar nan da kuma al’ummarta.

Ya kuma bayyana cewa dage binciken ya zama wajibi bisa la’akari da bukatar da ake da ita na kara tuntubar masu ruwa da tsaki a ciki da wajen harkar man fetur da kuma majalisun dokoki domin kara zurfafa bincike a kan lamarin.

Ya ce, “Abubuwan da ke faruwa a kasar nan da suka bukatar dukkanin masu ruwa da tsaki a harkokin gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya su dauki matakin gaggawa.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

“Yayin da muke matukar yin nadama kan duk wata matsala da ta shafi al’ummar kasar nan, an yanke wannan shawarar ne saboda amfanin kasa.”

Ya bayyana cewa an dauki kowanne daga cikin wadannan hukunce-hukuncen ne domin bai wa kwamitin wucin gadi damar gudanar da harkokin jin ra’ayoyin jama’a tare da samar da mafita mai dorewa kan kalubalen da ke fuskantar bangaren man fetur na kasar nan.

Majalisar dattawar ta kuma bai wa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa za a sanar da su sabuwar ranar jin ra’ayoyin jama’a nan gaba kadan.

Bincike ya nuna cewa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya kafa kwamitin wucin gadi da zai binciki biliyoyin da aka kashe wajen kula da matatun man kasar nan tare da binciko hukumomi da ke kula da kudaden da ake biya ga masu safara da kuma bankado zargin shigo da gurbatattun albarkatun man fetur da dizal mara inganci cikin kasar nan.

Wani bincike da aka yi ya nuna cewa kwamitin wucin gadi ya kammala gudanar da ayyukansa na bincike kafin ya gudanar da taron tattaunawa da shugabannin ma’aikatu da hukumomin da kuma wasu masu zaman kansu a bangaren man fetur na kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadakalaBincikeMaimajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliya: Uwargidan Gwamnan Yobe Ta Janjanta Wa Al’ummar Maiduguri 

Next Post

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Binciken
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

Wike Ya GargaÉ—i PDP Kan Bai Wa ÆŠan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.