• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Binciken Badakalar Mai

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Binciken

A yayin da jama’a ke nuna bacin rai da rashin gamsuwa sakamakon karin farashin man fetur da kuma karancinsa a kasuwanni, majalisar dattawa ta dakatar da binciken lamarin wanda ya haifar da rudani.

Jagoran majalisar dattawa kuma shugaban kwamitin binciken badakala a bangaren masana’antar man fetur ta Nijeriya, Sanata Opeyemi Bamidele ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a farkon makon nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Kaduna: Ruftawar Hanya Sakamakon Ambaliyar Ruwa Ta Katse Garuruwa Biyar A Lere 

A cikin sanarwar da Bamidele ya fitar bai yi bayanin dalilin dage binciken ba, amma ya yi ikirarin cewa an dauki matakin ne domin amfanar da kasar nan da kuma al’ummarta.

Ya kuma bayyana cewa dage binciken ya zama wajibi bisa la’akari da bukatar da ake da ita na kara tuntubar masu ruwa da tsaki a ciki da wajen harkar man fetur da kuma majalisun dokoki domin kara zurfafa bincike a kan lamarin.

Ya ce, “Abubuwan da ke faruwa a kasar nan da suka bukatar dukkanin masu ruwa da tsaki a harkokin gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya su dauki matakin gaggawa.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Yayin da muke matukar yin nadama kan duk wata matsala da ta shafi al’ummar kasar nan, an yanke wannan shawarar ne saboda amfanin kasa.”

Ya bayyana cewa an dauki kowanne daga cikin wadannan hukunce-hukuncen ne domin bai wa kwamitin wucin gadi damar gudanar da harkokin jin ra’ayoyin jama’a tare da samar da mafita mai dorewa kan kalubalen da ke fuskantar bangaren man fetur na kasar nan.

Majalisar dattawar ta kuma bai wa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa za a sanar da su sabuwar ranar jin ra’ayoyin jama’a nan gaba kadan.

Bincike ya nuna cewa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya kafa kwamitin wucin gadi da zai binciki biliyoyin da aka kashe wajen kula da matatun man kasar nan tare da binciko hukumomi da ke kula da kudaden da ake biya ga masu safara da kuma bankado zargin shigo da gurbatattun albarkatun man fetur da dizal mara inganci cikin kasar nan.

Wani bincike da aka yi ya nuna cewa kwamitin wucin gadi ya kammala gudanar da ayyukansa na bincike kafin ya gudanar da taron tattaunawa da shugabannin ma’aikatu da hukumomin da kuma wasu masu zaman kansu a bangaren man fetur na kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Binciken

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.