ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta dage taronta na kwamitin koli na kasa da na kwamitin zartarwa na kasa har zuwa wani lokaci.

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranakun 11 da 12 ga watan Satumba domin gudanar da tarukan kwamitoci guda biyu, biyo bayan amincewar da Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Aiki Tare Da Kasashen Duniya Wajen Sa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mutane Masu Bukata Ta Musamman
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutum 49 A Yankuna 226 A Kano — SEMA

Jam’iyyar ta kuma umurci mambobin kwamitocin guda biyu da su halarci taron.

ADVERTISEMENT

Sai dai sakataren yada labaran jam’iyyar APC na asa, Barista Felid Morka ya sanar da dage taron biyu a wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Litinin.

Sanarwar ta ce, “Ana sanar da mambobin kwamitin koli da na kwamitin zartarwa na kasa na jam’iyyar APC cewa, tarukan da aka shirya gudanarwa a ranakun 11 da 12 ga Satumba, 2024, an dage su har zuwa wani lokaci.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Jam’iyyar ba ta bayyana dalilan da ya sa ta dage tarukan ba, amma ana ganin cewa jam’iyyar ta dauki wannan mataki ne saboda shugaban kasa baya nan.

Babban sakataren jam’iyyar APC na kasa, Sanata Ajibola Basiru, ya bayyana cewa jam’iyyar APC za ta gudanar da babban tarukan ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Sakataren ya ce tarukan za su duba halin da jam’iyyar ke ciki da samar da hanyoyin magance kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta da zayyana wasu dabaru da za a aiwatarwa domin samun nasarar jam’iyyar.

Kwamitin koli na kasa na jam’iyyar APC ya kunshi dattawa da wasu daga cikin manyan jami’ai da shugabannin majalisa da masu mataimaka wa jam’iyyar wajen cimma matsaya kan batutuwan da za a tattauna a taron kwamitin zartarwa.

Haka kuma kwamitin na bayar da shawara ga jam’iyya da shugaban kasa.

Ana sa ran Shugaban Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima za su halarci tarukan.

Sauran wadanda ake sa ran za su halarci tarukan sun hada da manyan mambobin kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC (NWC), karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Ganduje, tsohon shugaban kasa da mataimakin shugaban kasa wadanda ’yan jam’iyya ne, manyan jami’ai na majalisar dokokin kasa na da da na yanzu, da tsaffin shugabannin jam’iyyar na kasa da sakatarorin jam’iyyar da jiga-jigan jam’iyyar guda biyu kowanne daga sassar kasar nan.

Basiru ya ce taron zai yi la’akari da rahoton binciken kudi na shekarar 2023/2024 tare da amincewa da kasafin kudin jam’iyyar na shekara mai zuwa.

Ya ce wani muhimmin abu a cikin ajandar taron shi ne, sake duba rajistar jam’iyyar APC, wanda ake sa ran zai kara kaimi ga mambobin jam’iyyar da kuma samar da sahihin bayanai game da adadin mambobin jam’iyyar a fadin kasar.

Ya kara da cewa, gabanin tarukan, jam’iyyar ta kaddamar da cibiyar ci gabanta a wani bangare na kokarin da take yi na gyara akidarta da kuma bayar da horo ga ‘ya’yan jam’iyyarta.

Basiru ya ce, “Taron zai kayyade ranar da za a gudanar da babban taron da ba na zabe ba. Babban taron kasa shi ne mafi girman tsarin yanke shawara na jam’iyyar. Muna da nau’i biyu na al’ada. Na farko shi ne, taron zabe. Bayan haka, muna kuma da babban taron tsakiyar wa’adi, wanda ba zababbu ba ne. Shugabannin jam’iyyar ne za su yanke hukunci kan haka.

“Tarukan za su sake duba zabukan da suka gabata da kuma da tsara yadda za a gudanar da zabukan Edo da Ondo, wanda za a yi a wannan watan da Nuwamba.”

Basiru ya ce bai san da rade-radin da ake yi cewa taron kwamitin zartarwa zai tantance makomar wasu jami’an jam’iyyar ba.

“Duk wani abu da ba a cikin ajandar tarukan ba mu sanan shi ba.”

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

'Yansanda sun Kama Masu Laifi 26, Sun Kwato Wayoyin Sata 126 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.