• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Umarci FIRS Ta Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 17 Na Haraji

by Abubakar Abba
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Majalisar Dattawa Ta Umarci FIRS Ta Dakatar Da Asarar Naira Tiriliyan 17 Na Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa, ta hanyar kwamtin kula da kudade na majalisar, ta nuna bacin ranta kan asarar da aka tabka ta Naira tiriliyan 17 biyo bayan damar da aka bayar wajen tattara haraji a shekaru biyar da suka gabata.

Kazalika, majalisar ta kuma shawarci hukumar tattara haraji ta FIRS da ta dakatar da bayar da wannan damar ta tattara harajin.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • ‘Yan bindiga Sun Kashe Mutum 6 A Jihar Katsina

Majalisar ta nuna kin aminta da ci gaba da bayar da wannan damar da majalisar ta yi, ta bijiro ne a cikin kasafin kudi na 2024 da hukumar ta FIRS ta gabatar wa da kwamitin kula da kashe kudade na majalisar.

Bugu da kari, shugaban hukumar  FIRS Zacch  Adedeji ya shda wa kwamtin cewa, hukumar na sa ran za ta tara harajin da ya kai jimlar Naira tiriliyan 19.4 a  2024, sabanin bashin harajin da ya kai Naira tiriliyan 2.7 wanda aka tsara za yi aikin yin hanyiyi da babban bankin Nijeriya zai yi a kasar nan, wanda kuma za a dakar da yin akin.

Shi ma a jwabinsa shugaban kwamitin sanata Sani Musa na jam’iyyar APC mai wakiltar mazabar Neja ta gabas ya shedawa shugaban na FIRS, cin zarafin na bayar da damar da biyan harajin, ya haifar da Nijeriya tabka asarar kimanin Naira tiriliyan 17 a shekaru biyar da suka wuce, wanda ya zama wajibi, a dakatar da bayar da wannan damar.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Ya yi nuni da cewa,  hasashen da shugaban hukumar ya yi na son tara harajin da ya kai na Naira tiriliyan 19 a 2024 abu ne mai kyau idan aka kwatanta da harajin da hukumar ta tara a 2023 wanda ya kai jimlar Naira 11.16.

Ya ci gaba da cewa, sai dai, majalisar na da yakinin za ka iya tara harajin da kai na Naira tiriliya 30 idan har an samar da matakan fa suka dace.

Har ila yau, Zacch ya shewa kwamitin cewa, don a kare Nijeriya daga rubanya karbar haraji FIRS ta hanyar uin hadaka da kwamtin da shugaban kasa Bola Tinubu ya kafa, za su rage karbar haraji da ban da ban da suka kai  62 zuwa guda 8, inda ya ce, wannan abun taiakici ne ganin cewa, a Niheriya  ayau ana karbar harajin da ya kai ba da ban da ban har guda 62 wanda kuma daga cikin 62, ya kai kashi 97 da ake iya tattarawa.

Ya kara da cewa, tuni kan wannan mun fara tuntubar gwamnonin jihohin kasar nan wanda ya zuwa yau, ba za mu samu sama da takwas zuwa tara na harajin da jihohi da gwamnatin tarayayya, za su tattara ba.

Da yake yin bayani kan takardamar wanzar da tsarin haraji na TCS na gina hanyoyi da CBN zai yi  Zacch ya nanata cewa, tun da farko an ware Naira tiriliyan 2.5 ne don yin aikin wanda kuma dole ne a wanzar da aikin, kafin a fara yin wani sabon aikin.

Kan shirin bashin haraji kuwa ya ce, shiri ne mai kyau amma dole ne sai kamfanin NNPCL ya kammala kashe Naira tiriliyan 2.5 da aka ware masa kafin a fara wani sabo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

Next Post

An Buga Jadawalin Zagaye Na 16 Na Gasar Europa Da UEFA Conference League

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

3 hours ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 week ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Next Post
An Buga Jadawalin Zagaye Na 16 Na Gasar Europa Da UEFA Conference League

An Buga Jadawalin Zagaye Na 16 Na Gasar Europa Da UEFA Conference League

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Majalisar Dattawa

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.