• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, ta sanar da dakatar da dan majalisa mai wakiltar mazabar Birnin Kebbi Arewa, Hon. Hassan Umar a zamanta na ranar Juma’a.

Wannan na cikin sanarwar manema labarai mai kwanan wata da ranar Juma’a 12 ga watan Afrilu, 2024, kuma mai dauke da sa hannun Suleiman Shamaki, magatakardan majalisar.

  • Kalau Nake Babu Abin Da Ke Damun Kwakwalwata – Adam Zango
  • Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 

Sanarwar ta bayyana cewar dan dakatar ne sakamakon wasu kalamai na rashin tsaro da ya yi, da kuma cin zarfi ga shugabancin majalisar kanta da ya haddasa rashin jituwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa a jihar.

Bisa ga wadanan zarge zargen ne majalisar dokokin Jihar ta bayar da sanarwar datakar da shi daga zaman majalisar ko gudanar da wani aiki har sai lokacin da majalisar ta bayar da sanarwar janye dakatarwar.

A wata tattaunawa da wasu daga cikin mutanen da dakatacen dan majalisar ke wakiltar a Mazabun Kola- Tarasa da Badariya sun bayyana lamarin da matukar bakin ciki, mummuna kuma a matsayin cin zarafi da kuma yin watsi da tanade-tanaden kundin tsarin mulki wanda ya bai wa kowace mazaba ikon wakilci ta samu mutum a matsayin mamba mai wakiltar wata mazabun a majalisar dokokin jiha ko a tarayya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Matakin da majalisar jihar ta dauka na dakatar da dan majalisarmu ba ya bisa ka’ida ta fuskar doka.”

Haka kuma sun jaddada cewa hakan bai dace da dimokuradiyya ba.

Haka zalika sun kara da cewa a iya saninsu wani zababben memba ba shi da ikon bisa ga kudin dokar tsarin mulki na dakatar da shi ko ita wanda aka zaba bisa cancanta a matsayin memba mai wakiltar wasu mazabun a yankin jiha ko na tarayya.

Al’ummar yankin dakatacen dan majalisar suna kira ga gwamnan jihar da shugabannin jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki da su gaggauta kawo karshen dakatarwar da aka yi masa.

Haka kuma, dakatarwar da aka yi masa gaba daya ya zama tauye hakkin daukacin mazabun Birnin Kebbi ta Arewa a majalisar kan wakiltar su, wanda ana nufin cewa a halin yanzu ba su da wakilci a zauren majalisar dokokin jihar.

“Bugu da kari muna ganin cewa hakan ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa kuma ba shi da tushe a gaban doka.

“Muna kira ga duk masu hannu da kuma ruwa da tsaki da su shigo tare da tabbatar da cewa an dawo da membanmu mai aiki tukuru ga mazabun Birnin Kebbi ta Arewa a majalisar dokokin Jiha.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hakimin Ikara, Injiniya Aminu Umar Ya Rasu

Next Post

Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

5 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

6 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

7 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

11 hours ago
Kebbi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

12 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

13 hours ago
Next Post
Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.