• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, ta sanar da dakatar da dan majalisa mai wakiltar mazabar Birnin Kebbi Arewa, Hon. Hassan Umar a zamanta na ranar Juma’a.

Wannan na cikin sanarwar manema labarai mai kwanan wata da ranar Juma’a 12 ga watan Afrilu, 2024, kuma mai dauke da sa hannun Suleiman Shamaki, magatakardan majalisar.

  • Kalau Nake Babu Abin Da Ke Damun Kwakwalwata – Adam Zango
  • Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 

Sanarwar ta bayyana cewar dan dakatar ne sakamakon wasu kalamai na rashin tsaro da ya yi, da kuma cin zarfi ga shugabancin majalisar kanta da ya haddasa rashin jituwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa a jihar.

Bisa ga wadanan zarge zargen ne majalisar dokokin Jihar ta bayar da sanarwar datakar da shi daga zaman majalisar ko gudanar da wani aiki har sai lokacin da majalisar ta bayar da sanarwar janye dakatarwar.

A wata tattaunawa da wasu daga cikin mutanen da dakatacen dan majalisar ke wakiltar a Mazabun Kola- Tarasa da Badariya sun bayyana lamarin da matukar bakin ciki, mummuna kuma a matsayin cin zarafi da kuma yin watsi da tanade-tanaden kundin tsarin mulki wanda ya bai wa kowace mazaba ikon wakilci ta samu mutum a matsayin mamba mai wakiltar wata mazabun a majalisar dokokin jiha ko a tarayya.

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

“Matakin da majalisar jihar ta dauka na dakatar da dan majalisarmu ba ya bisa ka’ida ta fuskar doka.”

Haka kuma sun jaddada cewa hakan bai dace da dimokuradiyya ba.

Haka zalika sun kara da cewa a iya saninsu wani zababben memba ba shi da ikon bisa ga kudin dokar tsarin mulki na dakatar da shi ko ita wanda aka zaba bisa cancanta a matsayin memba mai wakiltar wasu mazabun a yankin jiha ko na tarayya.

Al’ummar yankin dakatacen dan majalisar suna kira ga gwamnan jihar da shugabannin jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki da su gaggauta kawo karshen dakatarwar da aka yi masa.

Haka kuma, dakatarwar da aka yi masa gaba daya ya zama tauye hakkin daukacin mazabun Birnin Kebbi ta Arewa a majalisar kan wakiltar su, wanda ana nufin cewa a halin yanzu ba su da wakilci a zauren majalisar dokokin jihar.

“Bugu da kari muna ganin cewa hakan ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa kuma ba shi da tushe a gaban doka.

“Muna kira ga duk masu hannu da kuma ruwa da tsaki da su shigo tare da tabbatar da cewa an dawo da membanmu mai aiki tukuru ga mazabun Birnin Kebbi ta Arewa a majalisar dokokin Jiha.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hakimin Ikara, Injiniya Aminu Umar Ya Rasu

Next Post

Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

Related

Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba
Labarai

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

29 minutes ago
uba sani
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

1 hour ago
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu
Labarai

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

3 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da É—umi-É—uminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

4 hours ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

4 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

13 hours ago
Next Post
Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

September 5, 2025
uba sani

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

September 5, 2025
Manzon Allah

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

September 5, 2025
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

September 5, 2025
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Ministan Tsaro

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

September 5, 2025
Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.