ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, ta sanar da dakatar da dan majalisa mai wakiltar mazabar Birnin Kebbi Arewa, Hon. Hassan Umar a zamanta na ranar Juma’a.

Wannan na cikin sanarwar manema labarai mai kwanan wata da ranar Juma’a 12 ga watan Afrilu, 2024, kuma mai dauke da sa hannun Suleiman Shamaki, magatakardan majalisar.

  • Kalau Nake Babu Abin Da Ke Damun Kwakwalwata – Adam Zango
  • Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 

Sanarwar ta bayyana cewar dan dakatar ne sakamakon wasu kalamai na rashin tsaro da ya yi, da kuma cin zarfi ga shugabancin majalisar kanta da ya haddasa rashin jituwa tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa a jihar.

ADVERTISEMENT

Bisa ga wadanan zarge zargen ne majalisar dokokin Jihar ta bayar da sanarwar datakar da shi daga zaman majalisar ko gudanar da wani aiki har sai lokacin da majalisar ta bayar da sanarwar janye dakatarwar.

A wata tattaunawa da wasu daga cikin mutanen da dakatacen dan majalisar ke wakiltar a Mazabun Kola- Tarasa da Badariya sun bayyana lamarin da matukar bakin ciki, mummuna kuma a matsayin cin zarafi da kuma yin watsi da tanade-tanaden kundin tsarin mulki wanda ya bai wa kowace mazaba ikon wakilci ta samu mutum a matsayin mamba mai wakiltar wata mazabun a majalisar dokokin jiha ko a tarayya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Matakin da majalisar jihar ta dauka na dakatar da dan majalisarmu ba ya bisa ka’ida ta fuskar doka.”

Haka kuma sun jaddada cewa hakan bai dace da dimokuradiyya ba.

Haka zalika sun kara da cewa a iya saninsu wani zababben memba ba shi da ikon bisa ga kudin dokar tsarin mulki na dakatar da shi ko ita wanda aka zaba bisa cancanta a matsayin memba mai wakiltar wasu mazabun a yankin jiha ko na tarayya.

Al’ummar yankin dakatacen dan majalisar suna kira ga gwamnan jihar da shugabannin jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki da su gaggauta kawo karshen dakatarwar da aka yi masa.

Haka kuma, dakatarwar da aka yi masa gaba daya ya zama tauye hakkin daukacin mazabun Birnin Kebbi ta Arewa a majalisar kan wakiltar su, wanda ana nufin cewa a halin yanzu ba su da wakilci a zauren majalisar dokokin jihar.

“Bugu da kari muna ganin cewa hakan ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa kuma ba shi da tushe a gaban doka.

“Muna kira ga duk masu hannu da kuma ruwa da tsaki da su shigo tare da tabbatar da cewa an dawo da membanmu mai aiki tukuru ga mazabun Birnin Kebbi ta Arewa a majalisar dokokin Jiha.”

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

Babban Layin Tashar Wutar Lantarki Na Kasa Ya Sake Faduwa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.