ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 

by Sadiq
2 years ago
Iran

Duniya ta kira taron gaggawa domin nazari a kan hare-haren da Iran ta kai wa Isra’ila na ramuwar gayya, yayin da kasashen duniya ke bayyana damuwa dangane da barazanar barkewar yaki a tsakanin kasashen biyu.

Sakatare Janar na majalisar, Antonio Guterres, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana damuwa dangane da barazanar tabarbarewar al’amura a yankin gabas ta tsakiya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo

Shugabar gudanarwar kungiyar kasashen Turai, Ursula von der Leyen ta bukaci Iran da ta gaggauta tsagaita wuta da kuma kiran kasashen da su tsagaita wuta tare da aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya.

ADVERTISEMENT

Sakatare Janar na kungiyar kawancen tsaro ta NATO, Jens Stoltenberg ya ce sun yi Allah-wadai da abin da ya kira matakin na Iran, yayin da suke ci gaba da sanya ido a kan abin da ke faruwa.

Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak, ya bayyana harin na Iran a matsayin na rashin hankali, wanda ke iya fadada tashin hankalin da ke gudana a gabas ta tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Firaministan Canada Justin Trudeau ya soki harin na Iran, inda ya sake jaddada goyan bayan kasarsa ga Isra’ila.

Ita kuwa China ta bayyana harin na Iran a matsayin fadadar rikicin Gaza, inda ta bukaci aiwatar da kudirin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya domin tabbatar da tsagaita wuta da kuma kawo karshen rikicin.

China ta bukaci kasashen duniya musamman masu karfin fada a ji domin ganin sun taka rawar ganin wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin baki daya.

Kasar Masar ta bayyana matukar damuwa da tashin hankalin tare da bukatar taka-tsan-tsan domin kaucewa fadawa yaki.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi Allah-wadai da harin Iran a kan Isra’ila, wanda ya bayyana shi a matsayin abin da ka iya jefa daukacin yankin cikin tashin hankali.

Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz ya bayyana harin na Iran a matsayin rashin hankali.

Ita kuwa Rasha ta bayyana damuwa da harin, tare da samun taka-tsan-tsan, kamar yadda Qatar ta bukaci manyan kasashen duniya daukar matakin kwantar da hankalin bangarorin.

Kasar Saudi Arabiya ta yi kira ga bangarorin biyu da su kai zuciya nesa domin kare yankin gabas ta tsakiya.

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bayyana goyon bayansa ga Isra’ila bayan ganawa da manyan jami’an tsaron kasar, yayin da ya ce za su ci gaba da tallafa wa kasar.

Sauran kasashen da suka bayyana matsayi dangane da harin sun hada da Ukraine da Turkiya da Italiya da kuma Spain.

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi – Gwamna Nasir Idris

Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi - Gwamna Nasir Idris

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.