ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyin Kasashen Duniya Game Da Harin Da Iran Ta Kaddamar A Kan Isra’ila 

by Sadiq
2 years ago
Iran

Duniya ta kira taron gaggawa domin nazari a kan hare-haren da Iran ta kai wa Isra’ila na ramuwar gayya, yayin da kasashen duniya ke bayyana damuwa dangane da barazanar barkewar yaki a tsakanin kasashen biyu.

Sakatare Janar na majalisar, Antonio Guterres, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya bayyana damuwa dangane da barazanar tabarbarewar al’amura a yankin gabas ta tsakiya.

  • ‘Yansanda Sun Kama Tirelar Sata Da Kayan Miliyan 30 A Bauchi
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Yunƙurin Ƙwace Iko Da Sakatariyar Jihar Oyo

Shugabar gudanarwar kungiyar kasashen Turai, Ursula von der Leyen ta bukaci Iran da ta gaggauta tsagaita wuta da kuma kiran kasashen da su tsagaita wuta tare da aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya.

ADVERTISEMENT

Sakatare Janar na kungiyar kawancen tsaro ta NATO, Jens Stoltenberg ya ce sun yi Allah-wadai da abin da ya kira matakin na Iran, yayin da suke ci gaba da sanya ido a kan abin da ke faruwa.

Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak, ya bayyana harin na Iran a matsayin na rashin hankali, wanda ke iya fadada tashin hankalin da ke gudana a gabas ta tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Firaministan Canada Justin Trudeau ya soki harin na Iran, inda ya sake jaddada goyan bayan kasarsa ga Isra’ila.

Ita kuwa China ta bayyana harin na Iran a matsayin fadadar rikicin Gaza, inda ta bukaci aiwatar da kudirin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya domin tabbatar da tsagaita wuta da kuma kawo karshen rikicin.

China ta bukaci kasashen duniya musamman masu karfin fada a ji domin ganin sun taka rawar ganin wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin baki daya.

Kasar Masar ta bayyana matukar damuwa da tashin hankalin tare da bukatar taka-tsan-tsan domin kaucewa fadawa yaki.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi Allah-wadai da harin Iran a kan Isra’ila, wanda ya bayyana shi a matsayin abin da ka iya jefa daukacin yankin cikin tashin hankali.

Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz ya bayyana harin na Iran a matsayin rashin hankali.

Ita kuwa Rasha ta bayyana damuwa da harin, tare da samun taka-tsan-tsan, kamar yadda Qatar ta bukaci manyan kasashen duniya daukar matakin kwantar da hankalin bangarorin.

Kasar Saudi Arabiya ta yi kira ga bangarorin biyu da su kai zuciya nesa domin kare yankin gabas ta tsakiya.

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya bayyana goyon bayansa ga Isra’ila bayan ganawa da manyan jami’an tsaron kasar, yayin da ya ce za su ci gaba da tallafa wa kasar.

Sauran kasashen da suka bayyana matsayi dangane da harin sun hada da Ukraine da Turkiya da Italiya da kuma Spain.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi – Gwamna Nasir Idris

Zan Daga Darajar Wasanni A Kebbi - Gwamna Nasir Idris

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.