Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da kudurin dokar kafa hukumar samar da wutar lantarki ta jihar Kano ta shekarar 2025 ya zama doka.
Kudirin dai na neman samar da damammaki ga jihohin Kano, Katsina da Jigawa domin amfani da sauran hanyoyin samar da makamashi kamar na hasken rana da na iska da na ruwa domin amfanin al’ummarsu da kuma ci gaban jihohinsu.
- Artabu Tsakanin ‘Yan Bindiga Da ‘Yan Banga Ya Ci Rayuka Da Dama A Bauchi
- Manzon Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaba Nguema Na Gabon
Daukacin kwamatin majalisar ne ya amince da kudurin bayan karatu na uku da magatakardar majalisar, Bashir Diso ya karanta, yayin zaman majalisar na ranar Litinin wanda shugaban majalisar Rt. Hon. Ismail Falgore ya jagoranta.
Da yake karin haske game da abubuwan da aka tsara da kuma yadda hukumar za ta kasance, shugaban masu rinjaye na majalisar, Hon. Lawan Husseini ya shaidawa manema labarai cewa, sanya hannu kan dokar za ta kara samar da damarmakin wutar lantarki a jihohin uku.
Husseini ya jaddada cewa, za ta kuma rage wahalhalu da kuma rage tsadar makamashi ga ‘yan jihohin, za ta kuma samar wa kananan masana’antu da manyan masana’antu isasshen makamashi don yin kasuwanci, tare da bai wa asibitoci da cibiyoyin kula da ruwa damar gudanar da ayyuka yadda ya kamata.
Dangane da tsarin shugabancin hukumar da ake son yi, Husseini ya ce, za a samar da shugaba, manajan darakta da mataimakin manajan darakta wanda kowace jiha za ta samar da wakilai uku.
Ya kara da cewa, shugaban hukumar zai yi aiki na tsawon shekaru hudu wanda za a rika jujjuyawa a tsakanin jihohin da ke cikin tsarin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp