• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekara guda ke nan da aukuwar rikici tsakanin Ukraine da Rasha, rikicin da kawo yanzu ya haddasa miliyoyin ‘yan gudun hijira, baya ga kuma mummunan tasirin da ya haifar ta fannonin samar da abinci da makamashi da ma farfadowar tattalin arzikin duniya.

Da Rasha da Ukraine da ma sauran kasashen Turai da ke kusa da fagen yakin, har ma da sauran kasashen duniya da suka hada da na Afirka, duk sun dandana kudar rikicin, akasin yadda Amurka ke cin moriyar siyasa da mummunar riba ta hanyar samar da makamai.

  • Zaben 2023: ‘Yan Daba Sun Sace Na’urar BVAS 8 A Delta Da Katsina

Alkaluman da majalisar gudanarwar kasar Amurka ta samar sun nuna cewa, a shekarar kudi ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta sayar zuwa ketare ya karu da kimanin 50% bisa na shekarar 2021, kuma daya daga cikin dalilan haka shi ne barkewar rikici a tsakanin Ukraine da Rasha.

Kwanan baya, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya kai ziyara ta ba zata Ukraine, inda ya sanar da karin gudummawar soja da za su kai dala miliyan 500 da za ta samar wa Ukraine, kuma hakan na zuwa ne kasa da wata guda, bayan wata gudummawar soja da ta sanar a farkon wannan wata. Labarin da kamfanin dillancin labarai na AP ya bayar ya shaida cewa, gaba dayan gudummawar soja da Amurka ta samar wa Ukraine ya zarce dala biliyan 50.

A shekarar da ta gabata ce rikici ya barke tsakanin Ukraine da Rasha, sakamakon yadda Amurka ta rura wutar rikicin, yanzu haka, shugaban Amurka ya kara rura wutar a ziyararsa, a maimakon ya taimaka ga tabbatar da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

A yayin da ake cika shekara guda da aukuwar rikicin, ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayar da wata takarda a jiya, inda daga wasu fannoni 12 ta nanata matsayinta na daidaita matsalar Ukraine a siyasance, a cewarta, yin shawarwari shi ne hanya daya tilo wajen daidaita rikicin.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa, kasar Sin ta sha neman tabbatar da sulhu a tsakanin kasashen biyu. Ko da a kwanakin baya ma, ta yi shawarwari a kai tsaye da Ukraine da ma Rasha bi da bi, inda take kokarin neman sassauta mummunan yanayin da ake ciki.

A cikin shekarar da ta gabata, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, kuma hakan ya faru ne sakamakon irin ra’ayoyi na “zama lafiya da juna da martaba bambance-bambance” da “zama lafiya da kasa da kasa” da “kawar da yake-yake a duniya” da ke cikin al’adun gargajiya na tsawon tarihi na shekaru sama da 5000 na kasar Sin, ra’ayoyin da a zamanin yau aka bayyana su a cikin shawarar kiyaye tsaron duniya da kasar ta gabatar, wato a rika yin shawarwari a maimakon yin fito na fito, kuma a yi hadin gwiwa a maimakon kulla kawance, da ma cin moriyar juna a maimakon cin nasara daga faduwar wani bangare.

Matsalar Ukraine ta kara nunawa al’umma cewa, tsaro ba hakkin musamman na wasu kasashe ba ne, kuma bai kamata a lalata tsaron wata kasa don tabbatar da na wata ba, kuma habaka kawancen soja ba zai haifar da kome ba, illa ya lalata tsaron shiyya.

Makomar dan Adam daya ce. Tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya, ta yadda al’ummar kowace kasa za ta iya rayuwa cikin kwanciyar hankali da walwala, burinmu ne na bai daya. Duk wahalar da za a fuskanta, ya zama dole a daidaita matsalar Ukraine a siyasance. Aikin da muka sanya a gaba shi ne a tabbatar da tsagaita bude wuta a tsakanin kasashen biyu cikin gaggawa, kuma makamai ba za su tabbatar da zaman lafiya ba. (Mai zane:Mustapha Bulama)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 5 Sun Jikkata Yayin Da Boko Haram Suka Kai Hari Wajen Zabe A Borno

Next Post

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Daga Birnin Sin

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

41 minutes ago
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

19 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

21 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

22 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

23 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

2 days ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam'iyyar APC Na Kasa

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.