• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekara guda ke nan da aukuwar rikici tsakanin Ukraine da Rasha, rikicin da kawo yanzu ya haddasa miliyoyin ‘yan gudun hijira, baya ga kuma mummunan tasirin da ya haifar ta fannonin samar da abinci da makamashi da ma farfadowar tattalin arzikin duniya.

Da Rasha da Ukraine da ma sauran kasashen Turai da ke kusa da fagen yakin, har ma da sauran kasashen duniya da suka hada da na Afirka, duk sun dandana kudar rikicin, akasin yadda Amurka ke cin moriyar siyasa da mummunar riba ta hanyar samar da makamai.

  • Zaben 2023: ‘Yan Daba Sun Sace Na’urar BVAS 8 A Delta Da Katsina

Alkaluman da majalisar gudanarwar kasar Amurka ta samar sun nuna cewa, a shekarar kudi ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta sayar zuwa ketare ya karu da kimanin 50% bisa na shekarar 2021, kuma daya daga cikin dalilan haka shi ne barkewar rikici a tsakanin Ukraine da Rasha.

Kwanan baya, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya kai ziyara ta ba zata Ukraine, inda ya sanar da karin gudummawar soja da za su kai dala miliyan 500 da za ta samar wa Ukraine, kuma hakan na zuwa ne kasa da wata guda, bayan wata gudummawar soja da ta sanar a farkon wannan wata. Labarin da kamfanin dillancin labarai na AP ya bayar ya shaida cewa, gaba dayan gudummawar soja da Amurka ta samar wa Ukraine ya zarce dala biliyan 50.

A shekarar da ta gabata ce rikici ya barke tsakanin Ukraine da Rasha, sakamakon yadda Amurka ta rura wutar rikicin, yanzu haka, shugaban Amurka ya kara rura wutar a ziyararsa, a maimakon ya taimaka ga tabbatar da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

A yayin da ake cika shekara guda da aukuwar rikicin, ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayar da wata takarda a jiya, inda daga wasu fannoni 12 ta nanata matsayinta na daidaita matsalar Ukraine a siyasance, a cewarta, yin shawarwari shi ne hanya daya tilo wajen daidaita rikicin.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa, kasar Sin ta sha neman tabbatar da sulhu a tsakanin kasashen biyu. Ko da a kwanakin baya ma, ta yi shawarwari a kai tsaye da Ukraine da ma Rasha bi da bi, inda take kokarin neman sassauta mummunan yanayin da ake ciki.

A cikin shekarar da ta gabata, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, kuma hakan ya faru ne sakamakon irin ra’ayoyi na “zama lafiya da juna da martaba bambance-bambance” da “zama lafiya da kasa da kasa” da “kawar da yake-yake a duniya” da ke cikin al’adun gargajiya na tsawon tarihi na shekaru sama da 5000 na kasar Sin, ra’ayoyin da a zamanin yau aka bayyana su a cikin shawarar kiyaye tsaron duniya da kasar ta gabatar, wato a rika yin shawarwari a maimakon yin fito na fito, kuma a yi hadin gwiwa a maimakon kulla kawance, da ma cin moriyar juna a maimakon cin nasara daga faduwar wani bangare.

Matsalar Ukraine ta kara nunawa al’umma cewa, tsaro ba hakkin musamman na wasu kasashe ba ne, kuma bai kamata a lalata tsaron wata kasa don tabbatar da na wata ba, kuma habaka kawancen soja ba zai haifar da kome ba, illa ya lalata tsaron shiyya.

Makomar dan Adam daya ce. Tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya, ta yadda al’ummar kowace kasa za ta iya rayuwa cikin kwanciyar hankali da walwala, burinmu ne na bai daya. Duk wahalar da za a fuskanta, ya zama dole a daidaita matsalar Ukraine a siyasance. Aikin da muka sanya a gaba shi ne a tabbatar da tsagaita bude wuta a tsakanin kasashen biyu cikin gaggawa, kuma makamai ba za su tabbatar da zaman lafiya ba. (Mai zane:Mustapha Bulama)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 5 Sun Jikkata Yayin Da Boko Haram Suka Kai Hari Wajen Zabe A Borno

Next Post

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

10 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

11 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

13 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

14 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

21 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

23 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam'iyyar APC Na Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.