ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba

by CMG Hausa
3 years ago
Makamai

Shekara guda ke nan da aukuwar rikici tsakanin Ukraine da Rasha, rikicin da kawo yanzu ya haddasa miliyoyin ‘yan gudun hijira, baya ga kuma mummunan tasirin da ya haifar ta fannonin samar da abinci da makamashi da ma farfadowar tattalin arzikin duniya.

Da Rasha da Ukraine da ma sauran kasashen Turai da ke kusa da fagen yakin, har ma da sauran kasashen duniya da suka hada da na Afirka, duk sun dandana kudar rikicin, akasin yadda Amurka ke cin moriyar siyasa da mummunar riba ta hanyar samar da makamai.

  • Zaben 2023: ‘Yan Daba Sun Sace Na’urar BVAS 8 A Delta Da Katsina

Alkaluman da majalisar gudanarwar kasar Amurka ta samar sun nuna cewa, a shekarar kudi ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta sayar zuwa ketare ya karu da kimanin 50% bisa na shekarar 2021, kuma daya daga cikin dalilan haka shi ne barkewar rikici a tsakanin Ukraine da Rasha.

ADVERTISEMENT

Kwanan baya, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya kai ziyara ta ba zata Ukraine, inda ya sanar da karin gudummawar soja da za su kai dala miliyan 500 da za ta samar wa Ukraine, kuma hakan na zuwa ne kasa da wata guda, bayan wata gudummawar soja da ta sanar a farkon wannan wata. Labarin da kamfanin dillancin labarai na AP ya bayar ya shaida cewa, gaba dayan gudummawar soja da Amurka ta samar wa Ukraine ya zarce dala biliyan 50.

A shekarar da ta gabata ce rikici ya barke tsakanin Ukraine da Rasha, sakamakon yadda Amurka ta rura wutar rikicin, yanzu haka, shugaban Amurka ya kara rura wutar a ziyararsa, a maimakon ya taimaka ga tabbatar da zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

A yayin da ake cika shekara guda da aukuwar rikicin, ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayar da wata takarda a jiya, inda daga wasu fannoni 12 ta nanata matsayinta na daidaita matsalar Ukraine a siyasance, a cewarta, yin shawarwari shi ne hanya daya tilo wajen daidaita rikicin.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa, kasar Sin ta sha neman tabbatar da sulhu a tsakanin kasashen biyu. Ko da a kwanakin baya ma, ta yi shawarwari a kai tsaye da Ukraine da ma Rasha bi da bi, inda take kokarin neman sassauta mummunan yanayin da ake ciki.

A cikin shekarar da ta gabata, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, kuma hakan ya faru ne sakamakon irin ra’ayoyi na “zama lafiya da juna da martaba bambance-bambance” da “zama lafiya da kasa da kasa” da “kawar da yake-yake a duniya” da ke cikin al’adun gargajiya na tsawon tarihi na shekaru sama da 5000 na kasar Sin, ra’ayoyin da a zamanin yau aka bayyana su a cikin shawarar kiyaye tsaron duniya da kasar ta gabatar, wato a rika yin shawarwari a maimakon yin fito na fito, kuma a yi hadin gwiwa a maimakon kulla kawance, da ma cin moriyar juna a maimakon cin nasara daga faduwar wani bangare.

Matsalar Ukraine ta kara nunawa al’umma cewa, tsaro ba hakkin musamman na wasu kasashe ba ne, kuma bai kamata a lalata tsaron wata kasa don tabbatar da na wata ba, kuma habaka kawancen soja ba zai haifar da kome ba, illa ya lalata tsaron shiyya.

Makomar dan Adam daya ce. Tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya, ta yadda al’ummar kowace kasa za ta iya rayuwa cikin kwanciyar hankali da walwala, burinmu ne na bai daya. Duk wahalar da za a fuskanta, ya zama dole a daidaita matsalar Ukraine a siyasance. Aikin da muka sanya a gaba shi ne a tabbatar da tsagaita bude wuta a tsakanin kasashen biyu cikin gaggawa, kuma makamai ba za su tabbatar da zaman lafiya ba. (Mai zane:Mustapha Bulama)

 

 

Makamai
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam'iyyar APC Na Kasa

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.