• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malam Rabi’u Aminu Ya Zama Sabon Babban Limamin Jere

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Malam Rabi’u Aminu Ya Zama Sabon Babban Limamin Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin malaman da ke jagorantar wa’azozi da harkokin addinin Musulunci a yankin Karamar Hukumar Kagarko, Malam Muhammad Rabi’u Aminu da ke Unguwar Masukwani Jere, ya zama sabon babban limamin Masarautar Jere.

Wannan ya biyo bayan nada shi da mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya ya yi tare da mataimakansa guda biyu, limami na biyu, Malam Abubakar Idris Abubakar, da limami na uku Malam Is’hak Ibrahim Usman, a ranar Juma’a 10 ga Nuwambar 2023.

  • Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci ‘Yantar Da Falasdin
  • Sarkin Musulmi Ga Malamai: Ku Rika Shawartar Masu Mulki Kan Shugabanci Nagari

Da yake jawabi jim kadan bayan nadin, sabon babban limamin, Malam Muhammad Rabi’u, ya fara da cewa, “Farko muna godiya ga mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya kuma tare da du’ai, Allah ya saka masa da alkhairi, da cikin jama’a ya zabe mu, mu zama mu ne jagorori na limancin wannan gari. Muna fata Allah ya kara masa lafiya. Sannan muna masa ta’aziyyar babban limaminmu da muka rasa, Allah ya gafarta masa, Allah ya sa ya huta, Allah ya sa aljanna ce makomarsa.

“Kuma daga ciki muna godiya ga majalisar mai martaba Sarkin Jere, bisa gudunmawar da suka bayar don su ga cewa an zauna lafiya, an hada kai. Muna musu fatan alkhairi, da fatan Allah ya saka musu da alkhairi. Sannan ina tabbatar muku da cewa, ni da sauran limamai wadannan muna zaune lafiya, kanmu ya hadu. Kuma su malamaina ne, Allah ya saka musu da alkhairi.

“Daga cikin majalisar mai martaba Sarkin Jere akwai wani shiri da suka so su yi na hadin kan mutanen garin nan amma bai yiwu ba kuma da aka yi wannan tsarin na yanzu ba su ki ba, muna fatan Allah ya tabbatar da niyyarsu, Allah ya zaunar da mu lafiya ya saka musu da alkhairi.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

Malam Muhammad Rabi’u, ya yi kira ga sauran malamai su rika gyara musu idan sun ga kuskure cikin shugabancin harkokin addinin yankin da aka dora musu, yana mai cewa, “Duk abin da za mu yi na kuskure malamai su kira mu su gaya mana. Alhamdu lillah, daya daga cikin malamanu da ke irin wannan shi ne Malam Tanimu. Idan ya ji ka yi kuskure, zai kira ka a waje ya ce ina so zan yi maka gyara amma sai na zo, nakan ce a’a, ni ne zan zo, ba sau daya ba, ba sau biyu ba yana mana irin wannan gyara, Allah ya saka masa da alkhairi. A madadin wadannan limamai muna ma jama’ar musulmi godiya da suka ba mu goyon baya da hadin kai da fatan zaman lafiya. Allah ya zaunar da mu lafiya.” Ya bayyana.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya, ya yi kira ga sabon babban limamin da sauran mataimakansa su zama masu koyar da mutane a aikace ba da wa’azi da baki ba kawai, kana ya bukaci daukacin al’ummar masarautar su zama masu kyautata wa iyali da zaman lafiya.

“Addinin Musulunci da shi Allah zai mana hisabi gobe kiyama. Wanda ya ci jarrabawa ya tsira, wanda ya samu akasin haka kuma a uzu billahi. Ina kira ga limaman da muka nada yau su zama masu aikata abubuwan da suke wa’azi a kai, daga aiki ake so a rika koyarwa.Kuma ina kira ga daukacin al’ummmar Jere su zama musulmi na kirki da lyautata wa iyali da zaman lafiya. Kowa ya tsaya kan gaskiya, ban da dabi’u marasa kyau. Da ire-iren wadannan Allah zai dube mu da idon rahama ya sa mu a gidan Aljanna.” Ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babban limamin jereMalam Rabi'u Aminu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Editoci: Tinubu Ya Nemi ‘Yan Jarida Da Yaɗa Ingatattun Labarai Don Jawo Masu Zuba Jari A Nijeriya

Next Post

Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

Related

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

12 minutes ago
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu
Manyan Labarai

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

1 hour ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

2 hours ago
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

4 hours ago
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida
Manyan Labarai

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

5 hours ago
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

17 hours ago
Next Post
Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.