ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malam Rabi’u Aminu Ya Zama Sabon Babban Limamin Jere

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Jere

Daya daga cikin malaman da ke jagorantar wa’azozi da harkokin addinin Musulunci a yankin Karamar Hukumar Kagarko, Malam Muhammad Rabi’u Aminu da ke Unguwar Masukwani Jere, ya zama sabon babban limamin Masarautar Jere.

Wannan ya biyo bayan nada shi da mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya ya yi tare da mataimakansa guda biyu, limami na biyu, Malam Abubakar Idris Abubakar, da limami na uku Malam Is’hak Ibrahim Usman, a ranar Juma’a 10 ga Nuwambar 2023.

  • Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci ‘Yantar Da Falasdin
  • Sarkin Musulmi Ga Malamai: Ku Rika Shawartar Masu Mulki Kan Shugabanci Nagari

Da yake jawabi jim kadan bayan nadin, sabon babban limamin, Malam Muhammad Rabi’u, ya fara da cewa, “Farko muna godiya ga mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya kuma tare da du’ai, Allah ya saka masa da alkhairi, da cikin jama’a ya zabe mu, mu zama mu ne jagorori na limancin wannan gari. Muna fata Allah ya kara masa lafiya. Sannan muna masa ta’aziyyar babban limaminmu da muka rasa, Allah ya gafarta masa, Allah ya sa ya huta, Allah ya sa aljanna ce makomarsa.

ADVERTISEMENT

“Kuma daga ciki muna godiya ga majalisar mai martaba Sarkin Jere, bisa gudunmawar da suka bayar don su ga cewa an zauna lafiya, an hada kai. Muna musu fatan alkhairi, da fatan Allah ya saka musu da alkhairi. Sannan ina tabbatar muku da cewa, ni da sauran limamai wadannan muna zaune lafiya, kanmu ya hadu. Kuma su malamaina ne, Allah ya saka musu da alkhairi.

“Daga cikin majalisar mai martaba Sarkin Jere akwai wani shiri da suka so su yi na hadin kan mutanen garin nan amma bai yiwu ba kuma da aka yi wannan tsarin na yanzu ba su ki ba, muna fatan Allah ya tabbatar da niyyarsu, Allah ya zaunar da mu lafiya ya saka musu da alkhairi.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

Malam Muhammad Rabi’u, ya yi kira ga sauran malamai su rika gyara musu idan sun ga kuskure cikin shugabancin harkokin addinin yankin da aka dora musu, yana mai cewa, “Duk abin da za mu yi na kuskure malamai su kira mu su gaya mana. Alhamdu lillah, daya daga cikin malamanu da ke irin wannan shi ne Malam Tanimu. Idan ya ji ka yi kuskure, zai kira ka a waje ya ce ina so zan yi maka gyara amma sai na zo, nakan ce a’a, ni ne zan zo, ba sau daya ba, ba sau biyu ba yana mana irin wannan gyara, Allah ya saka masa da alkhairi. A madadin wadannan limamai muna ma jama’ar musulmi godiya da suka ba mu goyon baya da hadin kai da fatan zaman lafiya. Allah ya zaunar da mu lafiya.” Ya bayyana.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Jere, Alhaji Abdullahi Daniya, ya yi kira ga sabon babban limamin da sauran mataimakansa su zama masu koyar da mutane a aikace ba da wa’azi da baki ba kawai, kana ya bukaci daukacin al’ummar masarautar su zama masu kyautata wa iyali da zaman lafiya.

“Addinin Musulunci da shi Allah zai mana hisabi gobe kiyama. Wanda ya ci jarrabawa ya tsira, wanda ya samu akasin haka kuma a uzu billahi. Ina kira ga limaman da muka nada yau su zama masu aikata abubuwan da suke wa’azi a kai, daga aiki ake so a rika koyarwa.Kuma ina kira ga daukacin al’ummmar Jere su zama musulmi na kirki da lyautata wa iyali da zaman lafiya. Kowa ya tsaya kan gaskiya, ban da dabi’u marasa kyau. Da ire-iren wadannan Allah zai dube mu da idon rahama ya sa mu a gidan Aljanna.” Ya bayyana.

Jere
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya
Labarai

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Labarai

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Jere
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Next Post
Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

Kotu Ta Kori Karar Abba K. Yusuf Ta Tabbatar Da Hukuncin Kotun Zabe Da Ya Tabbatar Da Gawuna

LABARAI MASU NASABA

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Jere

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Jere

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Jere

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.