• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Man U Ta Maye Gurbin Eriksen Da Zai Yi Jinyar Watanni Uku

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Eriksen

Dan wasan tsakiyar kungiyar kwallon kafa ta Manchester United Christian Eriksen zai shafe akalla wata biyu yana jinya, bayan samun rauni a wasan kofin kalubale da suka buga da Reading ranar Asabar.

Sai dai kociyan kungiyar, Erik Ten Hag ya yi amanna cewa Manchester United na da ”yan wasa da za su iya cike gibin da Eriksen zai bari wanda hakan ya sa yake ganin ba shi da damuwa.

  • Shugaban Jam’iyyar NNPP Na Jihar Gombe Ya Koma APC Bayan Ganawarsa da Gwamna Inuwa

Ten Hag ya ce ranar karshe abu ne mai wahala a iya cike madadin dan wasa kuma a matsayinka na mai koyarwa ba za ka dauki mataki ba bagatatan saboda rauni, to amma kuma suna da ‘yan wasa a tsakiya kuma suna da kyau.

Dan wasan na Denmark ya buga wa Manchester United wasanni 31 a wannan kaka, bayan da ya rattaba hannu kan yarjejeniyar shekara uku kuma yana daya daga cikin ‘yan wasan da United take takama da su.

Kafin zuwan Eriksen Manchester United, ya yi kwallo a kungiyoyin Ajad da Tottenham da Inter Milan kafin ya tafi Brentford inda ya buga wasa a watanni shida kacal a kungiyar.
Watakila dan wasan tsakiyar ya iya kai wa har farkon watan Mayu kafin ya murmure, wato dab da a kare wannan kaka kenan kuma daman dan wasan kungiyar na tsakiya Donny Ban de Beek yana jiyya wanda ba zai dawo ba har sai bayan kammala wannan kaka.

LABARAI MASU NASABA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Sai dai kuma Manchester United din ta karbi aron dan wasa Marcel Sabitzer daga kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munich wanda zai zauna har zuwa karshen wannan kakar.

Dan wasan tsakiyar na Austria mai shekaru 28 zai maye gurbin Christian Eriksen ne da ke fama da doguwar jinya da kuma Scott Mc Tominay da shima ya samu rauni a baya-bayan nan.

Sabitzer wanda Munich ta sayo daga RB Leipzig lokacin ya na matsayin kyaftin wasanni 54 ya dokawa kungiyar ta Bundesliga daga sayensa a 2021 zuwa yanzu kuma a jawabinsa bayan rattaba hannu kan yarejejeniyar zaman aron a tawagar Eric ten hag, Sabitzer ya ce amsa tayin zuwa Old Trafford matsayin aro ne saboda ya san cikakkiyar dama ce gareshi ya bayar da gudunmawarsa ga gungiyar.

A tsawon lokacin da ya shafe yana buga wasa a turai Sabitner ya buga wasanni sau 443 a filayen wasa ya yinda a bangare guda ya buga wa kasar sa wasanni 68 tare da cin kwallaye 12.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax
Wasanni

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Next Post
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa'adin Karbar Tsofaffin Kudi

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.