• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manchester United Za Ta Yi Da-na-sanin Rabuwa Da Ni, Cewar Pogba

byAbba Ibrahim Wada
3 years ago
Pogba

Tsohon dan wasan kungiyar Manchester United, Paul Pogba ya ce yana son ya nuna wa Manchester United cewar ta yi kuskure da ba ta tsawaita kwantiraginsa ba a ci gaba da zaman kungiyar.

Wasu rahotanni na cewar Manchester United ta yi masa tayin fam 300,000 uku a kowanne mako domin ya ci gaba da buga mata wasa sai dai a wani shirin talbijin kan tarihin dan wasan da ake sayarwa a Amazon mai suna ‘The Pogumentary’, Pogba ya ce duk batun na ‘yaudara’ ne.

  • Abinda Yasa Ba Zan Zama Kocin Man U Ba – Zidane

Ana sa ran zai sake komawa Jubentus, bayan da ya bar United sakamakon karewar kwantiraginsa a kakar da aka kammala, sannan a shirin talbijin din na Pogba, wanda za a fara nunawa ranar Juma’a, dan wasan ya yi magana kan tsohon wakilinsa, Mino Raiola, wanda ya mutu bayan doguwar jinya a watan Afrilu.

Wani bidiyo da PA news ta gani daga tarihin Pogba ya ce yana son ya nuna wa Manchester United sun yi kuskure da suka ki bashi sabuwar yarjejeniya zai kuma nuna wa sauran kungiyoyi kuskuren da kungiyar ta yi na kin tsawaita zamansa da su.

Rahotanni dai sun bayyana cewa Manchester United ta yi wa Pogba dan Faransa tayin kwantiragi mai tsoka, amma ya ce a bidiyon ‘yaudara ce, sannan ya kara da cewa ta yaya za’a sanar da dan wasa kana bukatarsa, amma ba’a yi masa tayin yarjejeniyar tsawaita zamansa ba.

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Pogba, wanda ya fara buga Manchester United a makarantar horon ‘yan wasa matasa daga Le Habre yana da shekara 16 a 2009, an amince ya bar kungiyar a matakin wanda kwantaraginsa ya kare a 2012.

Sannan daga nan ya lashe gasar Serie A guda hudu a Jubentus daga nan ya sake komawa Manchester United kan kudi fam miliyan 89 a matakin wanda aka saya mafi tsada a duniya a watan Agustan 2016.

Shekara biyu tsakani ya taka rawar gani a gasar Kofin Duniya da ta kai Faransa ta lashe kofin a wasannin da Rasha ta karbi bakunci, sannan daga baya dangantaka ta yi tsami tsakanin Pogba da Jose Mourinho, kan rashin kwazonsa a lokacin wasanni da yawan jinya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Pogba

‘Yansanda Sun Yi Wa Masu Garkuwa Kofar Raggo, Suka Kwace AK-47 Da Harsasai A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version