• Leadership Hausa
Wednesday, September 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manchester United Za Ta Yi Da-na-sanin Rabuwa Da Ni, Cewar Pogba

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Manchester United Za Ta Yi Da-na-sanin Rabuwa Da Ni, Cewar Pogba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dan wasan kungiyar Manchester United, Paul Pogba ya ce yana son ya nuna wa Manchester United cewar ta yi kuskure da ba ta tsawaita kwantiraginsa ba a ci gaba da zaman kungiyar.

Wasu rahotanni na cewar Manchester United ta yi masa tayin fam 300,000 uku a kowanne mako domin ya ci gaba da buga mata wasa sai dai a wani shirin talbijin kan tarihin dan wasan da ake sayarwa a Amazon mai suna ‘The Pogumentary’, Pogba ya ce duk batun na ‘yaudara’ ne.

  • Abinda Yasa Ba Zan Zama Kocin Man U Ba – Zidane

Ana sa ran zai sake komawa Jubentus, bayan da ya bar United sakamakon karewar kwantiraginsa a kakar da aka kammala, sannan a shirin talbijin din na Pogba, wanda za a fara nunawa ranar Juma’a, dan wasan ya yi magana kan tsohon wakilinsa, Mino Raiola, wanda ya mutu bayan doguwar jinya a watan Afrilu.

Wani bidiyo da PA news ta gani daga tarihin Pogba ya ce yana son ya nuna wa Manchester United sun yi kuskure da suka ki bashi sabuwar yarjejeniya zai kuma nuna wa sauran kungiyoyi kuskuren da kungiyar ta yi na kin tsawaita zamansa da su.

Rahotanni dai sun bayyana cewa Manchester United ta yi wa Pogba dan Faransa tayin kwantiragi mai tsoka, amma ya ce a bidiyon ‘yaudara ce, sannan ya kara da cewa ta yaya za’a sanar da dan wasa kana bukatarsa, amma ba’a yi masa tayin yarjejeniyar tsawaita zamansa ba.

Labarai Masu Nasaba

Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

Rashford Ya Yi Hatsarin Mota A Hanyarsa Ta Zuwa Gida Bayan Tashi Daga Wasansu Da Burnley

Pogba, wanda ya fara buga Manchester United a makarantar horon ‘yan wasa matasa daga Le Habre yana da shekara 16 a 2009, an amince ya bar kungiyar a matakin wanda kwantaraginsa ya kare a 2012.

Sannan daga nan ya lashe gasar Serie A guda hudu a Jubentus daga nan ya sake komawa Manchester United kan kudi fam miliyan 89 a matakin wanda aka saya mafi tsada a duniya a watan Agustan 2016.

Shekara biyu tsakani ya taka rawar gani a gasar Kofin Duniya da ta kai Faransa ta lashe kofin a wasannin da Rasha ta karbi bakunci, sannan daga baya dangantaka ta yi tsami tsakanin Pogba da Jose Mourinho, kan rashin kwazonsa a lokacin wasanni da yawan jinya.

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Watsi Da Kusan Gonaki 500 Saboda ‘Yan Bindiga A Katsina -Mataimakin Gwamna

Next Post

‘Yansanda Sun Yi Wa Masu Garkuwa Kofar Raggo, Suka Kwace AK-47 Da Harsasai A Zamfara

Related

Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta
Wasanni

Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

7 hours ago
Rashford Ya Yi Hatsarin Mota A Hanyarsa Ta Zuwa Gida Bayan Tashi Daga Wasansu Da Burnley
Manyan Labarai

Rashford Ya Yi Hatsarin Mota A Hanyarsa Ta Zuwa Gida Bayan Tashi Daga Wasansu Da Burnley

2 days ago
Hasashen Yadda Wasan Arsenal Da Tottenham Zai Kaya
Wasanni

Hasashen Yadda Wasan Arsenal Da Tottenham Zai Kaya

3 days ago
Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya
Wasanni

Hasashe Yadda Wasan Manchester United Da Burnley Zai Kaya

4 days ago
Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl
Wasanni

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

4 days ago
Ten hag
Wasanni

Zan Shawo Kan Matsalar Da Ta Addabe Mu, In Ji Ten Hag

4 days ago
Next Post
Pogba

‘Yansanda Sun Yi Wa Masu Garkuwa Kofar Raggo, Suka Kwace AK-47 Da Harsasai A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe

Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe

September 26, 2023
NNPP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano Da Ta Ba Gawuna Nasara

NNPP Ta Kai Korafinta Ga Hukumar NJC Kan Kalaman Daya Da Cikin Alkalan Kotun Zaben Kano

September 26, 2023
Duniya

Ra’ayin Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ta Bai Daya Na Tattaro Karfin Sauya Duniya

September 26, 2023
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Tabbatar Da Sace Wasu Daliba A Jihar

September 26, 2023
JKS

Babban Jami’in JKS: Kasar Sin Za Ta Karfafa Hadin Gwiwa Da Amincewa Da Juna Da Kasar Masar

September 26, 2023
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

September 26, 2023
Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

September 26, 2023
Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

September 26, 2023
Kimiyya

Masana Kimiyya Na Kasashen Kenya Da Sin Sun Kaddamar Da Kundin Farko Game Da Nau’ikan Tsirran Da Kenya Ta Wallafa

September 26, 2023
Libya

Me Ya Haifar Da Ambaliya A Libya?

September 26, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.