• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kimanin manona 100 ne suka amfana da horon da  Cibiyar da ke kula da fitar da amfanin gona zuwa kasar waje NEPC ta gudanar  a karamar Obi da ke a jihar  Nasarawa.

An horas da manoman ne, kan dabarun zamani kan yadda za su fitar da Doyar da suka noma zuwa ketare.

  • Masanin Tattalin Arziki: Kasar Sin Ce Karfin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?

Jami’ar  hukumar da ke a ofishin karamar Cibiyar Lafia a cikin Amina Abdullahi Tumba ce ta kadamar da bayar da horon.

Horon na kwana daya, an bude shine a shalkwatar Agyaragu, sa ke a gundumar raya karkara ta  Jenkwe da ke a cikin jihar.

Aminca a hawabinta a wajen horon ta bayyana cewa, manufar horon da aka shirya wa manoman na Doyar a jihar ta Nasarawa, an shirya masu ne domin su zamo akan gaba a daukacin fadin kasar nan wajen yin noman na Doyar.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

A cewar Amina, jihar ta Nasarawa ta kasance ta na da kyakyawar kasa mai albarka wajen yin noma

Jami’ar ta kuma yi kira ga manoman na Doyar da suka amfana da dabarun  horon na noman na zamani lokacin horon su kara bunkasa nomansu na Doyar.

A kasidar da ya gabatar a wajen horon wani kwarare a fannin aikin noma William Akaamaa ya yi kira ga manoman na Doyar da ke a cikin jihar, da su dinga tuntubar kwararru a fannin aikin naoma ako da yaushe, musamman domin su kara habaka noman na sun a Doyar, da kuma aminta da ita a kasuwannin duniya.

A na sa bangaren Daraktan hukumar kula da ingancin abinci da magunguna NAFDAC reshen jihar Babatunji Omoyeri yay i jawabi ne akan mahimancin da ke tattare da fitar da amfanin gona zuwa kasuwanin duniya domin sayarwa

Babatunji  ya kuma shawarci manoman da su tabatar da suna bin dukkan ka’idojin da aka gindaya na fitar da Doyar da suka noma zuwa kasuwar duniya, musamna domin kar a dinga kin amincewa da ita idan an fitar da ita wajen.

Shi ma a na sa jawabin a gurin bayar da horon kwamishinan aikin noma da albarkatun Ruwa na jihar Nuhu Ibrahim Oshafu, godewa Cibiyar ta NEPC ya yi kan shiryawa manoman na Doyar horon.

Oshafu ya kuma bai wa Cibiyar tabbacin cewa, gwamnatin jihar a shirye take ta yi hadaka da Cibiyar, domin a kara bayar da kwarin guiwa wajen kara bunkasa noma a jihar musaman, ba wai noman  Doya kawai ba, har da sauran amfanin gona.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ManomaNasarawaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Peng Liyuan Ta Gana Da Uwargidan Shugaban Brazil

Next Post

An Hana ‘Yan Jarida Shiga Wajen Tattara Sakamakon Zabe A Adamawa

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

6 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

7 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
An Hana ‘Yan Jarida Shiga Wajen Tattara Sakamakon Zabe A Adamawa

An Hana 'Yan Jarida Shiga Wajen Tattara Sakamakon Zabe A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.