ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

by Sadiq
6 months ago
Jaririya

Wani manomi mai suna Malam Kabiru Kamba ya bayar da labarin yadda ya ceto wata jaririya da aka haifa tare da binne ta da ranta a gonarsa da ke Kamba, a karamar hukumar Dandi a Jihar Kebbi.

Ya bayar da wannan labari ne a ranar Litinin, lokacin da tawagar ƙungiyar da ke yaƙi da cin zarafin mata da yara (GBV) ta jihar ta kai masa ziyara a gidansa.

  • Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
  • Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Kabiru ya ce ya je gonarsa ne a ranar Juma’a, sai ya ga ƙasar wani ɓangare na gonar ta bambamta.

ADVERTISEMENT

Saboda mamakin lamarin, sai ya roƙi wasu masu babur da ke wucewa su taimaka masa ya tona wajen.

Yayin da suke tona ƙasar wajen, sai suka ga wani yadi a ciki.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Wannan ya tayar da masa hankali, sai ya kira ‘yansanda da ke kusa da wajen.

Bayan ‘yansanda sun zo sun tono ƙasar sosai, sai suka gano wata jaririya raye tana kuka, a naɗe cikin wani yadi.

Kabiru ya ce gwamnatin ƙaramar hukumar ta ba shi damar kula da jaririyar har sai ‘yansanda sun kammala bincike.

“Na yanke shawarar kula da jaririyar ne saboda jin-ƙai da imani da ɗan Adam. Matata ma kwanan nan ta haihu, don haka za ta shayar da jaririyar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za su raɗa wa jaririyar suna a ranar Laraba, kuma ya riga ya sayi rago da sauran kayayyakin buƙatar suna.

Matarsa ta ce ta ji daɗi kuma za ta karɓi jaririyar hannu biyu.

A lokacin ziyarar, Hajiya Rafa’atu Hammani, tsohuwar sakatariyar dindindin ta jihar, ta ce za ta kai rahoton lamarin ga matar gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab-Nasare Idris.

Sakataren ƙungiyar GBV, Alhaji Nasiru Idris, ya ce sun kai ziyarar ne domin nuna gode wa Kabiru saboda ceton rayuwar jaririyar, da kuma gode wa Allah.

Ya kuma yaba wa ‘yansanda saboda saurin ɗaukar mataki, tare da alƙawarin cewa za su ci gaba da tallafa wa jaririyar.

Tawagar ta bai wa jaririyar kayayyaki kamar su sabulai, kayan jarirai, madarar jarirai, katifa, gado, da kuma gidan sauro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina
Al'ajabi

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina

November 25, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.