ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Sin

Ga duk mai bibiyar harkokin da suka shafi kasar Sin sau da kafa, ba zai mance da yadda a yayin tarukan majalissar wakilan jama’ar kasar na NPC da majalissar bayar da shawara kan harkokin siyasa ta kasar CPPCC na bana, aka kaddamar da matakai daban daban na gyaran fuska ga manufofin kasar da suka shafi zamanantarwa irin ta Sin, tare da dora tubulin gina kasa a matakai na gaba. 

A idanunmu da muke nazartar hakan, kasar Sin na ta haye tarin kalubale, a kan turbarta ta bunkasa tattalin arziki, da kyautata zamantakewar al’umma da kare hakkokin bil Adama.

  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a watan Mayun shekarar 2023, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da a kara mayar da hankali sosai ga batun daidaita bunkasar yawan al’ummar kasar Sin da ingancin rayuwarsu bisa babban matsayi. Har ma ya jaddada bukatar hade fannonin zuba jari don samar da ababen more rayuwa da tabbatar da ribar gina al’umma a bayyane. Kuma a wannan shekara mun sake ganin bayyanar wannan manufa a zahiri, cikin rahoton aikin gwamnatin kasar Sin, wanda ya fayyace matukar bukatar samar da karin kudade da hidimomi domin cin gajiyar al’umma, matakin dake kara tabbatar da matsayin kasar Sin na mai kare hakkokin al’umma ta hanyar mayar da su gaban komai.

ADVERTISEMENT

Karkashin haka, kasar Sin ta tanadi tsare-tsare daban daban na kyautatawa al’umma, da suka hada da kyautata samar da guraben ayyukan yi mafiya dacewa da al’umma, da fadada bangarorin inshora ga ma’aikata, da saukaka damar samun nauo’in inshorar lafiya ga mazauna karkara, da mazauna birane da ba sa aiki, da rangwame kan hidimomin lafiya ga al’ummar kasa da sauran su.

Ko shakka babu a wannan zamani da neman tabbatuwar zaman lafiya, da ci gaba, da kare hakkin bil Adama suka zama burikan dukkanin sassan kasa da kasa, ma iya cewa kasar Sin ta ciri tuta, bisa kwazonta na neman hadin kan dukkanin kasashen duniya, ta yadda za a kai ga gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, tun daga kan batun yaki da talauci, da wanzar da zaman lafiya, zuwa shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da magance matsalolin kiwon lafiya dake addabar al’ummun duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Wannan hazaka, da hangen nesa na kasar Sin, sun ci gaba da zama ginshiki na ingiza jagorancin dukkanin manufofin kare hakkin bil Adama a duniya, kana hakan zai ci gaba da zama muhimmiyar gudummawar kasar Sin ga duniya, a bangaren kare hakkin rayuwa da walwalar daukacin al’ummar duniya.(Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.