• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar harkokin da suka shafi kasar Sin sau da kafa, ba zai mance da yadda a yayin tarukan majalissar wakilan jama’ar kasar na NPC da majalissar bayar da shawara kan harkokin siyasa ta kasar CPPCC na bana, aka kaddamar da matakai daban daban na gyaran fuska ga manufofin kasar da suka shafi zamanantarwa irin ta Sin, tare da dora tubulin gina kasa a matakai na gaba. 

A idanunmu da muke nazartar hakan, kasar Sin na ta haye tarin kalubale, a kan turbarta ta bunkasa tattalin arziki, da kyautata zamantakewar al’umma da kare hakkokin bil Adama.

  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a watan Mayun shekarar 2023, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da a kara mayar da hankali sosai ga batun daidaita bunkasar yawan al’ummar kasar Sin da ingancin rayuwarsu bisa babban matsayi. Har ma ya jaddada bukatar hade fannonin zuba jari don samar da ababen more rayuwa da tabbatar da ribar gina al’umma a bayyane. Kuma a wannan shekara mun sake ganin bayyanar wannan manufa a zahiri, cikin rahoton aikin gwamnatin kasar Sin, wanda ya fayyace matukar bukatar samar da karin kudade da hidimomi domin cin gajiyar al’umma, matakin dake kara tabbatar da matsayin kasar Sin na mai kare hakkokin al’umma ta hanyar mayar da su gaban komai.

Karkashin haka, kasar Sin ta tanadi tsare-tsare daban daban na kyautatawa al’umma, da suka hada da kyautata samar da guraben ayyukan yi mafiya dacewa da al’umma, da fadada bangarorin inshora ga ma’aikata, da saukaka damar samun nauo’in inshorar lafiya ga mazauna karkara, da mazauna birane da ba sa aiki, da rangwame kan hidimomin lafiya ga al’ummar kasa da sauran su.

Ko shakka babu a wannan zamani da neman tabbatuwar zaman lafiya, da ci gaba, da kare hakkin bil Adama suka zama burikan dukkanin sassan kasa da kasa, ma iya cewa kasar Sin ta ciri tuta, bisa kwazonta na neman hadin kan dukkanin kasashen duniya, ta yadda za a kai ga gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, tun daga kan batun yaki da talauci, da wanzar da zaman lafiya, zuwa shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da magance matsalolin kiwon lafiya dake addabar al’ummun duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

Wannan hazaka, da hangen nesa na kasar Sin, sun ci gaba da zama ginshiki na ingiza jagorancin dukkanin manufofin kare hakkin bil Adama a duniya, kana hakan zai ci gaba da zama muhimmiyar gudummawar kasar Sin ga duniya, a bangaren kare hakkin rayuwa da walwalar daukacin al’ummar duniya.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Yaba Wa Majalisar Dokoki Kan Amincewa Da Dokar Ta-Ɓaci A Jihar Ribas

Next Post

Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

Related

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

7 hours ago
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025
Daga Birnin Sin

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

8 hours ago
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
Daga Birnin Sin

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

9 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

10 hours ago
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici
Daga Birnin Sin

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

13 hours ago
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

14 hours ago
Next Post
Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.