ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Ga duk mai bibiyar harkokin da suka shafi kasar Sin sau da kafa, ba zai mance da yadda a yayin tarukan majalissar wakilan jama’ar kasar na NPC da majalissar bayar da shawara kan harkokin siyasa ta kasar CPPCC na bana, aka kaddamar da matakai daban daban na gyaran fuska ga manufofin kasar da suka shafi zamanantarwa irin ta Sin, tare da dora tubulin gina kasa a matakai na gaba. 

A idanunmu da muke nazartar hakan, kasar Sin na ta haye tarin kalubale, a kan turbarta ta bunkasa tattalin arziki, da kyautata zamantakewar al’umma da kare hakkokin bil Adama.

  • Wa Ke Dandana Kudar Matakin Harajin Kwastan Da Gwamnatin Amurka Ta Dauka
  • El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a watan Mayun shekarar 2023, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira da a kara mayar da hankali sosai ga batun daidaita bunkasar yawan al’ummar kasar Sin da ingancin rayuwarsu bisa babban matsayi. Har ma ya jaddada bukatar hade fannonin zuba jari don samar da ababen more rayuwa da tabbatar da ribar gina al’umma a bayyane. Kuma a wannan shekara mun sake ganin bayyanar wannan manufa a zahiri, cikin rahoton aikin gwamnatin kasar Sin, wanda ya fayyace matukar bukatar samar da karin kudade da hidimomi domin cin gajiyar al’umma, matakin dake kara tabbatar da matsayin kasar Sin na mai kare hakkokin al’umma ta hanyar mayar da su gaban komai.

ADVERTISEMENT

Karkashin haka, kasar Sin ta tanadi tsare-tsare daban daban na kyautatawa al’umma, da suka hada da kyautata samar da guraben ayyukan yi mafiya dacewa da al’umma, da fadada bangarorin inshora ga ma’aikata, da saukaka damar samun nauo’in inshorar lafiya ga mazauna karkara, da mazauna birane da ba sa aiki, da rangwame kan hidimomin lafiya ga al’ummar kasa da sauran su.

Ko shakka babu a wannan zamani da neman tabbatuwar zaman lafiya, da ci gaba, da kare hakkin bil Adama suka zama burikan dukkanin sassan kasa da kasa, ma iya cewa kasar Sin ta ciri tuta, bisa kwazonta na neman hadin kan dukkanin kasashen duniya, ta yadda za a kai ga gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, tun daga kan batun yaki da talauci, da wanzar da zaman lafiya, zuwa shawo kan kalubalen sauyin yanayi, da magance matsalolin kiwon lafiya dake addabar al’ummun duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Wannan hazaka, da hangen nesa na kasar Sin, sun ci gaba da zama ginshiki na ingiza jagorancin dukkanin manufofin kare hakkin bil Adama a duniya, kana hakan zai ci gaba da zama muhimmiyar gudummawar kasar Sin ga duniya, a bangaren kare hakkin rayuwa da walwalar daukacin al’ummar duniya.(Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

Sin: Shingayen Kasuwanci Suna Illata Wadatar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.