• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanaki ne wata kungiya mai zaman kanta mai suna ‘Centre for the Promotion of Pribate Enterprise (CPPE)’ ta aika wa sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, (CBN), Michael Olayemi Cardoso, wasika inda ta zayyana wasu matakai guda 10 da ya kamata a dauka da gaggawa in har ana son a dawo da tattalin arzikin kasa a hayyacinsa.

A daidai lokacin da yake shiga ofis a mastayin shugaban Babban Bankin Nijeriya zai fuskanci matsaloli da dama da suke addabar tattalin arzikin kasa wadanda suka hada da hauhawar farashi, hauhawar kudin ruwa, karyewar darajar bankuna, karyewar darajar naira, sune kuma za su zama masa gwaji na farko da zai fuskanta a matsayinsa na jagoran Babban Bankin Nijeriya. Babu wani kokwanto na cewa, lallai Cardoso ya cancanci zama shugaban babban banki musammna ganin irin kwarewar da yake da shi a bangaren ayyukan da suka shafi tattalin arzik a baya.

  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas
  • Takardun Karatun Tinubu Ba Na Bogi Ba Ne – Fadar Shugaban Kasa

Hanyar farko da ya kamata ya dauka na fuskantar wadanna matsaloli shi ne, kamar yadda kungiyar ta bayyana, ya sake fasalin bangaren bankunan kasar nan, wannan a cewar su yana da muhimmanci, don shi ne zai dawo da karfin gwiwar masu zuba jari wanda hakan kuma zai taimaka wajen daga darajar Naira da take ta fadi kasa warwas ‘yan shekarun nan. Sake fasalin Naira da tsohon gwamnan babban banki, Godwin Emeifele ya aiwatar ya haifar da matsaloli da dama, ya kuma kamata a gaggauta daukar matakin dakile matsalolin da hakan ya haifar ga bunkasar tattalin arzikin Nijeriya.

Sauran matsalolin sun kuma hada da duba wa’adin shugabancin bankuna da kuma irin kudaden da ya kamata su mallaka na jari don gudanar da ayyukansu, da kuma bukatar nemo hanyoyin hada kai da manyan kamfanonin kasa da na kasashen waje don bunkasa bangaren bankunan Nijeriya.

Yana kuma da matukar muhimmanci a fahinci cewa, Cardoso ya dare karagar jagorancin Babban Bankin Nijeriya ne a daidai wani lokaci mai muhimmanci a tarihin tattalin arzikin kasa. Ba sai mun fada ba, akwai rudani mai girma a bangaren musayar kudaden waje a kasar nan, abin da ya haifar da gagrumin karyewar darajar Naira a kasuwannin duniya. Haka kuma bangaren tattalin arzikin kasa na fama karyewar darajar naira wanda hakan kuma ya haifar da hauhawar farashin albarkatun Man Fetur da na kayan masarufi da ake amfani dasu yau da kullum, akwai kuma bukatar gaggawa na karfafa yadda ake biyan Ruwan basukan da ke bin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Bangaren harkokin kula da tattalin arzikin kasa sun girgiza da manufofin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bullo da su, a saboda haka ya zama doke shugaban Babban Bankin Nijeriya ya samar da wasu manufofi da za su kwantar wa masu zuba jari na ciki da wajen kasa hankali don su ci gaba da hulda da Nijeriya ba tare da wata fargaba ba, ta hanyar daukar matakin farfado da darajar Naira da kuma rage kudaden ruwa a basukan da ake ba masu kanana da matsakaitan masana’antu.

Haka kuma, akwai bukatar shugabannin babban banki a karkashin jagorancin sabbon shugabansu su duba bangaren shiga da fitar da kayayyaki a kasar nan don  samar da yanayin da bankuna za su shigo don samar da kudade ga masu kasuwanci a ciki da wajen kasar nan a cikin sauki ba tare da ruwa mai tsanani ba, ta wannan hanyar naira za ta samar wa kanta daraja a fagen kasuwannin duniya.

Ya kamata a dauki darasi daga kamfanonin jiragen sama a kasar nan inda a halin yanzu suke duba wasu bangarori na tattalin arziki don tattabatar da wanzuwarsu a fagen gwagwarmayar kasuwanci, a kan haka bangaren tattalin arzaiki masu zaman kansu suka yi kira ga gwamnati da ta waiwayi wannan bangarn don a karfafa zuciyar masu zuba jari na ciki da kasashen waje.

Shugaban kungiyar da ta yi wannan bincike tare da bayar da wadanna shawarwarin, Dakta Muda Yusuf, ya kara bayar da haske, inda ya bayyana cewa, akwai bukatar a kara daga kudin jari bankuna daga Naira biliyan 2 zuwa Naira Biliyan 25, yana mai cewa, tun shekarar 2004 aka yi wa jarin da bankuna ke amfani da shi kwaskwarima, matsalar da aka fuskanta kuma yana faruwa ne saboda faduwar darajar naira a kasuwannin duniya.

A kan haka, kara darajar jarin bankuna yana da matukar muhimmanci saboda karin jari ga bankuna zai daidata harkokin bankuna da tattalin arzikin kasa, haka kuma kungiyar ta nemi a dakatar da shirin sake wa naira fasali gaba daya saboda babu wani kwakkwarar dalilin yin haka tun da farko.

Haka kuma kafin wannan lokacin, masu manyan masana’antu a kasar nan sun nemi a kawo musu dauki ta hanyar rage ruwan da ake karba a bankuna na basukan da suke karbar don bunkasa harkokinsu, wannan zai karfafa kokarin da gwamnati take yi na mayar da hankali ga wasu bangarori da ba na albarkatun mai ba wajen samo wa kasa kudaden shiga.

Masana na da ra’ayin cewa, gibin da ke tsakanin kudin ruwan da ake karba da kudin da ake ajiiyewa a bankuna yana da fadin gaske wanda hakan yana nuna irin matsalar da ake fuskanta kenan a bangaren harkokin bankunan kasar nan. A kan haka suka yi kira ga sabon gwamna babban bankin ya gaggauta daukan matakin daidaita wannan gibin don samar da ci gaban da ake bukata a bangaren kanana da matsaikaitan masana’antun Nijeriya.

A ra’ayinmu kuma, ya kamata Cardoso ya dauki matakin ceto bangaren kamfanoni masu zaman kansu, daga dukkan alamu yanayin da ake ciki bai basu daman walwala da bunkasa yadda ya kamata ba.

Ganin irin dimbin sanin makaman aiki na sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya, Cardoso, da kuma irin bayanan da ya yi a gaban majalisar dattawa a yayin da ake tantance shi, muna da kwarin gwiwar cewa, za a samu canjin da ake bukkata na kai Babban Bankin Nijeriya matsayin da ya dace da shi, a kan haka muke yi masa fatan alhairi a kan wannan gagarumin aikin da zai fuskanta a shekaru masu zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Samar Da Fasfo 204,332 Cikin Mako Uku – Adepoju

Next Post

Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

Related

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

16 hours ago
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 
Manyan Labarai

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

1 day ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

2 days ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 
Da É—umi-É—uminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

3 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

3 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

3 days ago
Next Post
Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

Sabon Salon 'Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami'a Mata...

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.