ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
Manyan

A kwanaki ne wata kungiya mai zaman kanta mai suna ‘Centre for the Promotion of Pribate Enterprise (CPPE)’ ta aika wa sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, (CBN), Michael Olayemi Cardoso, wasika inda ta zayyana wasu matakai guda 10 da ya kamata a dauka da gaggawa in har ana son a dawo da tattalin arzikin kasa a hayyacinsa.

A daidai lokacin da yake shiga ofis a mastayin shugaban Babban Bankin Nijeriya zai fuskanci matsaloli da dama da suke addabar tattalin arzikin kasa wadanda suka hada da hauhawar farashi, hauhawar kudin ruwa, karyewar darajar bankuna, karyewar darajar naira, sune kuma za su zama masa gwaji na farko da zai fuskanta a matsayinsa na jagoran Babban Bankin Nijeriya. Babu wani kokwanto na cewa, lallai Cardoso ya cancanci zama shugaban babban banki musammna ganin irin kwarewar da yake da shi a bangaren ayyukan da suka shafi tattalin arzik a baya.

  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas
  • Takardun Karatun Tinubu Ba Na Bogi Ba Ne – Fadar Shugaban Kasa

Hanyar farko da ya kamata ya dauka na fuskantar wadanna matsaloli shi ne, kamar yadda kungiyar ta bayyana, ya sake fasalin bangaren bankunan kasar nan, wannan a cewar su yana da muhimmanci, don shi ne zai dawo da karfin gwiwar masu zuba jari wanda hakan kuma zai taimaka wajen daga darajar Naira da take ta fadi kasa warwas ‘yan shekarun nan. Sake fasalin Naira da tsohon gwamnan babban banki, Godwin Emeifele ya aiwatar ya haifar da matsaloli da dama, ya kuma kamata a gaggauta daukar matakin dakile matsalolin da hakan ya haifar ga bunkasar tattalin arzikin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Sauran matsalolin sun kuma hada da duba wa’adin shugabancin bankuna da kuma irin kudaden da ya kamata su mallaka na jari don gudanar da ayyukansu, da kuma bukatar nemo hanyoyin hada kai da manyan kamfanonin kasa da na kasashen waje don bunkasa bangaren bankunan Nijeriya.

Yana kuma da matukar muhimmanci a fahinci cewa, Cardoso ya dare karagar jagorancin Babban Bankin Nijeriya ne a daidai wani lokaci mai muhimmanci a tarihin tattalin arzikin kasa. Ba sai mun fada ba, akwai rudani mai girma a bangaren musayar kudaden waje a kasar nan, abin da ya haifar da gagrumin karyewar darajar Naira a kasuwannin duniya. Haka kuma bangaren tattalin arzikin kasa na fama karyewar darajar naira wanda hakan kuma ya haifar da hauhawar farashin albarkatun Man Fetur da na kayan masarufi da ake amfani dasu yau da kullum, akwai kuma bukatar gaggawa na karfafa yadda ake biyan Ruwan basukan da ke bin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Bangaren harkokin kula da tattalin arzikin kasa sun girgiza da manufofin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bullo da su, a saboda haka ya zama doke shugaban Babban Bankin Nijeriya ya samar da wasu manufofi da za su kwantar wa masu zuba jari na ciki da wajen kasa hankali don su ci gaba da hulda da Nijeriya ba tare da wata fargaba ba, ta hanyar daukar matakin farfado da darajar Naira da kuma rage kudaden ruwa a basukan da ake ba masu kanana da matsakaitan masana’antu.

Haka kuma, akwai bukatar shugabannin babban banki a karkashin jagorancin sabbon shugabansu su duba bangaren shiga da fitar da kayayyaki a kasar nan don  samar da yanayin da bankuna za su shigo don samar da kudade ga masu kasuwanci a ciki da wajen kasar nan a cikin sauki ba tare da ruwa mai tsanani ba, ta wannan hanyar naira za ta samar wa kanta daraja a fagen kasuwannin duniya.

Ya kamata a dauki darasi daga kamfanonin jiragen sama a kasar nan inda a halin yanzu suke duba wasu bangarori na tattalin arziki don tattabatar da wanzuwarsu a fagen gwagwarmayar kasuwanci, a kan haka bangaren tattalin arzaiki masu zaman kansu suka yi kira ga gwamnati da ta waiwayi wannan bangarn don a karfafa zuciyar masu zuba jari na ciki da kasashen waje.

Shugaban kungiyar da ta yi wannan bincike tare da bayar da wadanna shawarwarin, Dakta Muda Yusuf, ya kara bayar da haske, inda ya bayyana cewa, akwai bukatar a kara daga kudin jari bankuna daga Naira biliyan 2 zuwa Naira Biliyan 25, yana mai cewa, tun shekarar 2004 aka yi wa jarin da bankuna ke amfani da shi kwaskwarima, matsalar da aka fuskanta kuma yana faruwa ne saboda faduwar darajar naira a kasuwannin duniya.

A kan haka, kara darajar jarin bankuna yana da matukar muhimmanci saboda karin jari ga bankuna zai daidata harkokin bankuna da tattalin arzikin kasa, haka kuma kungiyar ta nemi a dakatar da shirin sake wa naira fasali gaba daya saboda babu wani kwakkwarar dalilin yin haka tun da farko.

Haka kuma kafin wannan lokacin, masu manyan masana’antu a kasar nan sun nemi a kawo musu dauki ta hanyar rage ruwan da ake karba a bankuna na basukan da suke karbar don bunkasa harkokinsu, wannan zai karfafa kokarin da gwamnati take yi na mayar da hankali ga wasu bangarori da ba na albarkatun mai ba wajen samo wa kasa kudaden shiga.

Masana na da ra’ayin cewa, gibin da ke tsakanin kudin ruwan da ake karba da kudin da ake ajiiyewa a bankuna yana da fadin gaske wanda hakan yana nuna irin matsalar da ake fuskanta kenan a bangaren harkokin bankunan kasar nan. A kan haka suka yi kira ga sabon gwamna babban bankin ya gaggauta daukan matakin daidaita wannan gibin don samar da ci gaban da ake bukata a bangaren kanana da matsaikaitan masana’antun Nijeriya.

A ra’ayinmu kuma, ya kamata Cardoso ya dauki matakin ceto bangaren kamfanoni masu zaman kansu, daga dukkan alamu yanayin da ake ciki bai basu daman walwala da bunkasa yadda ya kamata ba.

Ganin irin dimbin sanin makaman aiki na sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya, Cardoso, da kuma irin bayanan da ya yi a gaban majalisar dattawa a yayin da ake tantance shi, muna da kwarin gwiwar cewa, za a samu canjin da ake bukkata na kai Babban Bankin Nijeriya matsayin da ya dace da shi, a kan haka muke yi masa fatan alhairi a kan wannan gagarumin aikin da zai fuskanta a shekaru masu zuwa.

Manyan
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

Sabon Salon 'Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami'a Mata...

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.