ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

by Bello Hamza
3 years ago
Salon

A halin yanzu kungiyoyin dalibai da na matasa sun fara gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da kuma nuna bukatar su na a gaggauta ceto dalibai ‘yan mata na Jami’o’in Gwamnatin Tarayya da ke Gusau da Dutsimma wadanda ‘yan ta’adda suka sace. Zanga-zangar da ake gudana a kafafen sadarwa na zamani (Soshiyal Mediya), yana samun karbuwa, don har wasu Jaruman masana’antar Kannywood kamar Ali Nuhu sun shiga tare da nuna goyon bayansu a kan bukatar a kawo karshen sace-sacen dalibai a manyan makarantu. Wannan gangami yana neman ya yi kama da salon da wasu kungoyi suka dauka shekarun baya a lokacin da aka sace dalibai mata na makarantar sakandari n agarin Chibok da ke Jihar Borno (#birngbackourgirls) wanda ya samu karbwa a sassan duniya ciki har da Shugaba Amurka na wanncan lokacin, Barak Obama.

Wannan yana nuna harzukar da matasa suka a yankin arewa a kan haren-haren ‘yan ta’addan a mayan makarantu. Don ko a ranar Laraba tun bayan da ‘yan bindiga suka shiga dakunan kwanan dalibai mata na jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau Jihar Zamfara, gwamnatin jihar da jami’an tsaro suke ta fadi tashin ganin an ceto dukkan wadanda aka sace.

  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas
  • Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku

 Gwamna Jihar a Dauda Lawal ya a ta bakin mai magana da yawunsa, Alhaji Sulaiman Bala Idris, ya ce, gwamnatin jihar na ba jami’an tsaro dukkan goyon bayan da suke bukata na ganin an ceto daliban a cikin koshin lafiya. Wannan ne ma ya haifar da takaddama a tsakanikn gwamnatin jihar da jami’an gwamnatin tarayya inda ake zargin wasu jami’an gwamnatin tarayya na gudanar da tattaunawar sulhu da ‘yan ta’adda ba tare da sanin gwamnatin jihar ba, abin da gwamnatin tarayya da karyata.

ADVERTISEMENT

Bayan kwashe awanni muna tattaunawa kan harkar tsaro, a yau na kaddamar da kwamitin da zai fara aiki don samar da Rundunar Kare Garuruwa (Community Protection Guard).

Wannan yana daga cikin shirinmu don tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Babban aikin wannan kwamiti shi ne samar da tsari wanda da shi za a kafa wannan rundunar ta CPG, don mu iya ba da kariya ga garuruwanmu baki daya.

Aiki ne babba, amma da yardar Allah za mu yi nasara.

Babu gudu, ba ja da baya a kudurinmu na kawo karshen ‘yan bindiga. A dalilin haka nake sake nanata cewa ba za mu yi sulhu da mabarnata ba.

A na cikin jamamin sace daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya na Gusau ne sai kuma gashi ranar Laraba 4 ga watan Oktoba 2023 a ka samu labarin sace wasu dalibai mata 5 a Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Dutsin-ma ta Jihar Katsina.

Bayanai sun tabbatar da cewa, an sace daliban ne daga dakuna  kwanan su da ke ‘Mariamoh Ajiri Memorial International School’ da misalin karfe 2:30 na daren Laraba, jami’in watsa labarai na rundunar ‘yansandan jihar Katsina, ASP Abubakar Sadik Aliyu, ya tabbatar da labarin ya kuma ce an samu nasarar kama wasu da ake zargi da hannu a sace daliban kuma a na ci gaba da gudanar da bincike don sanin yadda za a ceto su.

Wannan tashin hankalin ya sa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu   umarci jami’an tsaro su gaggauuta ceto sauran daliban da suke hannun ‘yan ta’addan ba tare da bata lokaci ba, bayan an samu nasarar ceto dalibai 7 a samamamen da ‘yansanda suka yi a cikin daji, musamman ganin jami’ar mallakin gamnatin tarayya ne.

Jami’in watsa labaran shugaban kasa, Ajuri Ngelale, ya yi tir da sace ‘yan matan, yana mai kara da cewa, babu wani dalili na sace yaran, wanda laifin su klawai shi ne na kokarin zuwa makartanta neman ilimi.

Shugaban kasar ya mika jajensa ga iyalai da ‘yanuwan daliban, yana mai tabbatar musu da cewa, gwamnati za ta tabbatar da cetosu tare da dawo da su a cikin iyalansu cikin koshin lafiya.

Tinubu ya kuma yi alkawarin tabbatar da tsaro a dukkan manyan makarantun kasar nan, don dukkan ‘yan kasa su damar samun ingantaccen ilimi a fadin tarayya kasar nan.

Wannan barazana ne ga ilijmin mata

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta bayyana yadda ake sace-sacen dalibai ‘yan mata a manyan makarantumu a mastayin barazana ga kokarin ilimantar da yara mata a arewacin Nijeriya.

Sun bukaci gwamnatin tarayya ta hada kan rundunonin tsaron kasar nan don fito da sabbin hanyoyin kare makarantunmu daga wannan matsalar wanda yake neman zama babbar barazana ga ci gaban yankin arewa da ma Nijeriya gaba daya.

ACF ta bayyana haka ne a takardar sanarwar da sakatarenta na kasa, Farfesa Tukur Muhammad Baba ya sanya wa hannu, ya kuma kara da cewa, ya kamata gwamnati ta yi dukkan kokarin da ya kamata na ganin an ceto daliban ba tare da wani cutarwa ba.

Sanarwar ta kuma kara dacewa, “ACF ta yi tir da wannnan lamarin da kakkausar murya musamman ganin wannan ba shi ba ne na farko a yankin arewa ba kuma wani abu ne da ya kamata a tir da shi a dukka fadin duniya.

“Lamarin yana tayar da hankali ne musamman ganin yana iya durkushe kokarin da ake yi na karfafa harkar ilimin mata a Nijeriya, wanda dama yana fuskantar manyan matsaloli a ‘yan shekarun nan.

“Wannan yana da tayar da hankali in aka lura da yadda wasu iyaye suke shirin janye yaransu mata daga manyan makarantu da yadda wasu ke canza shirin su na zabar wasu jami’o’i saboda yadda yankin ke fuskantar matsalar tsaro.”

Haka kuma shugabban kungiyar ‘Amnesty Int’I reshen Nijeriya,

Isa Sanusi, ya nemi a gudanar da cikakken bincike a kan yadda aka sace daliban Jami’ar Gusau da kuma sauran sace-sacen ‘yan mata a manyan makarantun yankin arewa gaba daya. Ya kuma nemi a dauki dukkan matakai na shari’a don ganin an ceto yaran ba tare da bata lokaci ba.

Sanusi ya kuma kara da cewa, “Ya kamata makarantu su zama waje mai aminci bai kamata su fuskanci barazana da tashin hankali ba a yayin da suke neman ilimi. Jami’an gwamnati sun bayyana cewa, sun shawwo kan matsalar tsaro a yankin arewa amma ayyukan ‘yan ta’adda yana nuna cewa kamar labarin ba haka yake ba.”

“Hari tare da sace dalkibain a jami’o’in gwamnatin tarayya na Gusau wani babban laifi ne da ya shafi kasa da kasa yana kuma neman kawo cikas ga akokarin bayar da ilimi wanda hakki ne ga dukkan bil’adam.

“Daga dukkan alamu hukumomi basu dauki darasin da ya kamata ba a yadda ake sace dalibai a makarantu a sassan yankin arewa, wannan sace-sacen da ake yi na baya bayan yana nuna cewa, ba a yi wani tsari ba na kare dalibai daga wannan annobar na sace daliba da kuma kare aukuwar irin haka a gaba.

“Dole gwamnatin Nijeriya ta gudanar da binicike na musamman don hukunta duk wani da ke da sakaci a faruwar wannan lamarin.

Salon
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da 'Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.