• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Najeriya Sun Amince Da Ci Gaban Hadin Kai Karkashin Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

by CGTN Hausa
2 years ago
Najeriya

Wasu kasashen yamma sun dade suna karawa batun bashin da Sin take baiwa Afrika gishiri, musamman ma bayan an gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, sun bayyana bashin da Sin take baiwa kasashen Afirka a matsayin abin da zai haifar da matsalar bashi.

Irin wannan kalamai na cewa wai bashin da Sin take baiwa Afrika tarko ne, na da nufin hana bunkasuwar hadin kan Sin da Afirka da cin moriya tare.

  • Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus
  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Sinawa na da wani karin magana dake nuna cewa, idan ana son tabbatar da ganin bunkasuwar tattalin arziki, dole ne a fara ne da gina hanyoyi. Shi ya sa, rancen kudin da Sin take baiwa Najeriya wajen aiwatar da ayyukan hadin gwiwa karkashin wannan shawara ta “ziri daya da hanya daya”, yawancinsu ana amfani da su wajen samar da manyan ababen more rayuwa. Alal misali, an gina layin dogo na farko mai amfani da ma’aunin Sin a Afrika, wato layin dogo dake tsakanin Abuja da Kaduna a Najeirya, da kuma layin dogo na farko dake cikin birni a yammacin Afirka, wato layin dogo na Abuja na Najeirya.

A can baya tsohon shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari ya taba shaidawa manema labarai cewa, rancen kudin da Sin take baiwa Najeriya, an yi amfani da su ne wajen gina layin dogo, da hanyoyin mota da dai sauransu, kuma idan babu irin wadannan ayyuka, al’ummar kasar ba yadda za su yi sai su yi zirga-ziraga da kafafu. Ya kuma yi maraba da duk wata kasa dake iya baiwa kasarsa taimako a fannin gina manyan ababen mora rayuwa.

Amma shin me ya hana wadannan kasashen yamma?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

A farkon watan bara na kai ziyara a Najeriya, na kuma zanta da kakakin majalisar wakilan tarayyar Nijeriya Abbas Tajudeen, kuma yayin zantawar mu ya ce, kasashe da dama suna shirin baiwa Najeriya rancen kudi, amma kasashen Afrika suna zabar rancen da ya dace da yanayin da suke ciki. Idan an kwatanta da manufofin sauran kasashe, rancen kudin da Sin ta samar na kunshe da kudin ruwa mai araha, da wa’adi mai tsawo. Najeriya na godiya sosai kan taimakon da Sin take ba ta wajen raya tattalin arzikinta. Ban da wannan, bisa rahotannin da wasu hukumomin kasa da kasa, da kungiyoyin nazari suka bayar, an ce, yawancin basusukan da kasashen Afirka suke karba na fitowa ne daga daidaikun mutane na kasashen yamma.

Kasashen Afrika na da ma’ auninsu na zabar abokan hadin gwiwa, bisa la’akari da moriyarsu. A halin yanzu, karin kasashe sun karbi shawarar “ziri daya da hanya daya”. Alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta dauka game da hadin gwiwar shawarar daddade ne, kuma ya dace da muradunsu, shi ya sa ta samu amincewa daga kasashe, da jama’arsu da suka karbi shawarar. Ban da wannan kuma, rancen kudin da Sin take baiwa kasashen, ana amfani da su ne wajen gina manyan ababen more rayuwa, matakin da zai ingiza bunkasuwar tattalin arzikinsu. Kaza lika idan an yi hangen nesa, za a ga cewa zai taimakawa wadannan kasashe wajen biyan bashin da kasashen yamma, da wasu hukumomin kudaden kasa da kasa suke binsu. (Mai zana da rubuta: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

Yadda Uwargida Za Ta Hada Boga

LABARAI MASU NASABA

Najeriya

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.