• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu sanaar kiwon kifi a Nijeriya, na ci gaba da samun matsaloli ta fuskar koma baya tare da durkushewa a wannan sanaa tasu. Akwai manya-manyan dalilai da suke taka muhimmiyar rawa wajen durkushewar masu wannan sanaa a Nijeriya.

-Rashin Samun Kasuwa: Masu sanaar kiwon Kifi na fara wa ne da neman kasuwar da za su sayar da Kifin da suka kiwata, domin matsalar ita ce, a yayin da suke ci gaba da ciyar da su, Kwamin da suke kiwata su na adadin da zai iya dauka na yawan kifayen, ba sa wani kara ci gaba da yin girma.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Malamin Addini Da Sassan Mutum Danye A Oyo
  • Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka

-Haka zalika, zabo gidan gonar da babu wadataccen ruwan da za a rika shayar da su, rashin kasa mai inganci da za a kafa kwamin kiwon Kifin da sauransu, na da matukar amfani wajen yin laakari.

-Sannan, gina kwami na siminti maras inganci wanda zai iya hujewa da rashin ba shi kuwalwar da ta dace, ba karamar matsala ba ce. Akwai kuma rashin daukar kwararrun maaiktan da za su rinka kwashe kifayen zuwa wani kwamin daban da sauran makamantansu.

-Sai kuma batun rashin tsara sanya hannun jari, wanda mafi yawan masu yin kiwon na tunanin kafin shiga cikin sanaar, sai sun tanadi kwamin kiwon masu yawa, wanda hakan ke sanya su kafa kwami masu yawan gaske a lokaci guda, inda hakan ke sanya wasu shafe tsawon lokaci ba tare da sun fara yin kiwon ba.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

-Haka nan rashin sanin ilimin yin kiwon, domin kuwa ana son duk wanda zai fara sanaar ya kasance ya samu ilimin shiga sanaar kafin ya fara aiwatar da ita.

-Rashin daukar maaikatan da ba su dace ba, shi ma na matukar taimakawa wajen durkushewar wannan sanaa. Dalili kuwa, wadansu na daukar yanuwansu wadanda ba su da ilimi a wannan fanni a matsayin maaikatansu, inda hakan ke zame masu wani nauyi, sannan su gaza sallamar su daga wannan aiki, koda kuwa ba sa yi musu aikin yadda ya kamata ba.

-Har wa yau, rashin zuwan manajoji masu lura da gidan gonar, shi ma ba karamar matsala ba ce, domin kuwa kiwon Kifayen daga nesa ko kuma ta hanyar buga waya, domin bayar da umarni ga maaikata, ko shakka babu zai iya shafar tafiyar da gidan gonar.

-Rashin ciyar da su abincinsu yadda ya dace, shi ma na kawo nakasu ga wannan sanaa kai tsaye. Domin kuwa, rashin ilimi a kan abincin da zai rika gina wa Kifayen jiki, matsala ce mai zaman kanta. Dalili kuwa, da yawa daga cikin masu kiwon na sayen abincin ne mai rahusa, domin rage kashe kudade masu yawa. Bugu da kari, wasu masu kiwon ba sa lura da irin yanayin da kifayen nasu ke ciki tare da yanayin sauyin da suka samu, domin ba a cin kifi da ba shi da lafiya

-Gazawar daukar maaikatan da suka dace, don ciyar da kifayen tare da lura da yadda yanayin girman kifayen yake lokaci zuwa lokaci.

-Sai kuma batun rashin sanin yadda za a bai wa kifayen lulawa, ta yadda wasu masu gidan gonar kiwon kifayen, ba sa daukar maaikatan da suka dace; wadanda za su rika kula musu da kifayen yadda ya kamata.

-Mayar da hankali a kan kifaye yan kadan da ake kiwatawa, mai makon kifayen baki-daya, wannan ma wata babbar nakasu ce ga masu sanaar.

-Sannan, rashin adana bayanai da kuma rashin tantance kokarin da ake yi a kan kiwon, kan sanya su gaza sanin adadin ribar da suke samu ko kuma asarar da suka yi.

-Yin Kiwo a masayin shaawa, na sanya wa masu kiwon gaza kwashe kifayen da suka riga suka kammala girma a kan lokaci, inda suke ganin kamar suna kiwata manyan dabbobi ne a babban Kogi.

-Rashin Kwakkwarar manufa ta yin kiwon, ita ma na taka muhimmiyar rawa wajen durkushewar masu yin wannan sanaa, domin kuwa wasu na shiga cikin harkar ne kawai, domin ganin wasu abokansu na yi ko kuma burin samun wani tallafi daga wurin gwamnati.

-Akwai kuma batun sake fadada giraman kiwon kifayen, sakamakon rashin samun riba mai yawa da kuma rashin samun kifaye masu yawa. Wannan ba kasuwanci ne mai kyau ba, domin kuwa abin da ya fi dacewa shi ne, lalubo da mafita a kan matsalar da ta sanya mai sanaar kiwon ke gazawa, don yin gyara a kansu.

-Abu na karshe shi ne, yin ammana da rahotannin da jaridu da masu tuntuba suka wallafa na cewa, ana bukatar kudade yan kadan ne kawai a matsayin jari, a samu kazamar riba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KiwoKiwon kaji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Noman Kadanya: Yadda Rashin Amfani Da Fasahar Zamani Ke Dakile Samun Dimbin Riba

Next Post

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

16 hours ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 day ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

2 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

3 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

1 week ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

1 week ago
Next Post
Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.