ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kalubalen Da Ke Durkusar Da Kiwon Kifi A Nijeriya

by Abubakar Abba
3 years ago
Kiwon kifi

Masu sanaar kiwon kifi a Nijeriya, na ci gaba da samun matsaloli ta fuskar koma baya tare da durkushewa a wannan sanaa tasu. Akwai manya-manyan dalilai da suke taka muhimmiyar rawa wajen durkushewar masu wannan sanaa a Nijeriya.

-Rashin Samun Kasuwa: Masu sanaar kiwon Kifi na fara wa ne da neman kasuwar da za su sayar da Kifin da suka kiwata, domin matsalar ita ce, a yayin da suke ci gaba da ciyar da su, Kwamin da suke kiwata su na adadin da zai iya dauka na yawan kifayen, ba sa wani kara ci gaba da yin girma.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Malamin Addini Da Sassan Mutum Danye A Oyo
  • Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka

-Haka zalika, zabo gidan gonar da babu wadataccen ruwan da za a rika shayar da su, rashin kasa mai inganci da za a kafa kwamin kiwon Kifin da sauransu, na da matukar amfani wajen yin laakari.

ADVERTISEMENT

-Sannan, gina kwami na siminti maras inganci wanda zai iya hujewa da rashin ba shi kuwalwar da ta dace, ba karamar matsala ba ce. Akwai kuma rashin daukar kwararrun maaiktan da za su rinka kwashe kifayen zuwa wani kwamin daban da sauran makamantansu.

-Sai kuma batun rashin tsara sanya hannun jari, wanda mafi yawan masu yin kiwon na tunanin kafin shiga cikin sanaar, sai sun tanadi kwamin kiwon masu yawa, wanda hakan ke sanya su kafa kwami masu yawan gaske a lokaci guda, inda hakan ke sanya wasu shafe tsawon lokaci ba tare da sun fara yin kiwon ba.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

-Haka nan rashin sanin ilimin yin kiwon, domin kuwa ana son duk wanda zai fara sanaar ya kasance ya samu ilimin shiga sanaar kafin ya fara aiwatar da ita.

-Rashin daukar maaikatan da ba su dace ba, shi ma na matukar taimakawa wajen durkushewar wannan sanaa. Dalili kuwa, wadansu na daukar yanuwansu wadanda ba su da ilimi a wannan fanni a matsayin maaikatansu, inda hakan ke zame masu wani nauyi, sannan su gaza sallamar su daga wannan aiki, koda kuwa ba sa yi musu aikin yadda ya kamata ba.

-Har wa yau, rashin zuwan manajoji masu lura da gidan gonar, shi ma ba karamar matsala ba ce, domin kuwa kiwon Kifayen daga nesa ko kuma ta hanyar buga waya, domin bayar da umarni ga maaikata, ko shakka babu zai iya shafar tafiyar da gidan gonar.

-Rashin ciyar da su abincinsu yadda ya dace, shi ma na kawo nakasu ga wannan sanaa kai tsaye. Domin kuwa, rashin ilimi a kan abincin da zai rika gina wa Kifayen jiki, matsala ce mai zaman kanta. Dalili kuwa, da yawa daga cikin masu kiwon na sayen abincin ne mai rahusa, domin rage kashe kudade masu yawa. Bugu da kari, wasu masu kiwon ba sa lura da irin yanayin da kifayen nasu ke ciki tare da yanayin sauyin da suka samu, domin ba a cin kifi da ba shi da lafiya

-Gazawar daukar maaikatan da suka dace, don ciyar da kifayen tare da lura da yadda yanayin girman kifayen yake lokaci zuwa lokaci.

-Sai kuma batun rashin sanin yadda za a bai wa kifayen lulawa, ta yadda wasu masu gidan gonar kiwon kifayen, ba sa daukar maaikatan da suka dace; wadanda za su rika kula musu da kifayen yadda ya kamata.

-Mayar da hankali a kan kifaye yan kadan da ake kiwatawa, mai makon kifayen baki-daya, wannan ma wata babbar nakasu ce ga masu sanaar.

-Sannan, rashin adana bayanai da kuma rashin tantance kokarin da ake yi a kan kiwon, kan sanya su gaza sanin adadin ribar da suke samu ko kuma asarar da suka yi.

-Yin Kiwo a masayin shaawa, na sanya wa masu kiwon gaza kwashe kifayen da suka riga suka kammala girma a kan lokaci, inda suke ganin kamar suna kiwata manyan dabbobi ne a babban Kogi.

-Rashin Kwakkwarar manufa ta yin kiwon, ita ma na taka muhimmiyar rawa wajen durkushewar masu yin wannan sanaa, domin kuwa wasu na shiga cikin harkar ne kawai, domin ganin wasu abokansu na yi ko kuma burin samun wani tallafi daga wurin gwamnati.

-Akwai kuma batun sake fadada giraman kiwon kifayen, sakamakon rashin samun riba mai yawa da kuma rashin samun kifaye masu yawa. Wannan ba kasuwanci ne mai kyau ba, domin kuwa abin da ya fi dacewa shi ne, lalubo da mafita a kan matsalar da ta sanya mai sanaar kiwon ke gazawa, don yin gyara a kansu.

-Abu na karshe shi ne, yin ammana da rahotannin da jaridu da masu tuntuba suka wallafa na cewa, ana bukatar kudade yan kadan ne kawai a matsayin jari, a samu kazamar riba.

Kiwon kifi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

Hadarin Mota: NIS Ta Tabbatar Da Mutuwar Jamianta 4, 7 Sun Ji Rauni A Kano

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.