• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
2 months ago
Manzon Allah

Annabi Muhammad (SAW) jinkai ne ga halitta baki daya saboda fadin Ubangiji, “wa ma arsalnaka illa rahmatan lil alamin – ba a aiko ka ba sai don ka zama rahama ga halitta”. Ya tabbata a hadisai ingantattu cewa, Manzon Allah (SAW), shi ne mai ceton halitta ranar Alkiyama, kamar yadda Alkur’ani ya tabbatar da fadinsa, “Asa an yab’asaka rabbuka makaman Mahmuda”.

Annabi (SAW), shi ne shugaban ‘ya’yan Annabi Adamu duka. Tun daga kan Annabi Adam zuwa na karshen ‘ya’yansa, duka za su kasance a karkashin tutar shugabancin Annabi (SAW) a ranar Alkiyama.

Annabi (SAW) shi ne cikamakon Annabawa kuma jagoransu, komai ya zo da shi, babu wani abu sabo da za a zo da shi, sai dai na Annabi (SAW) ne za a yi ta warware wa. Ko dai ya warware mana wata mas’ala da ba a fahimce ta ba ko kuma ya zo da wata sabuwar fahimta amma dai tana cikin abin da Annabi (SAW) ya zo da shi. Ita ce wannan ilimin kimiyya da fasaha da muke gani yanzun.

Addinin Annabi (SAW) shi ne mafificin Addinatai, duk da cewa sauran addinatan daga Ubangiji suke, amma ba kamar nasa. Al’ummar Annabi (SAW) ita ce mafificiyar al’umma. Babu yadda za a yi wannan al’umma ta zama mafificiyar al’umma amma annabinta bai zama mafificin Annabawa ba.

Littafin Manzon Allah (SAW) Alkur’ani, shi ne mafificin Littattafai, ya kunso Ilimai da sanin Allah. Shehu Ibrahim Inyass (RA), ya ce “Alkur’ani ya yi maganar kowanne fanni, duk wani dan fanni ya dauki maganar fanninsa a cikin Alkur’ani. Alkur’ani ba waka ba ne, wanda ya kawo shi ba mawaki ba ne, amma Larabci ne. Kowane harshe, yana da wake, amma Larabawa sun yi wake da yawa, don haka, akwai gurbinta a Alkur’ani.

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW), shi ne farkon wanda kasa za ta tsage wa ya tashi a ranar Alkiyama, shi ne farkon wanda zai shiga Aljannah, shi ne wanda Allah ya kebanta da tsani da wasilah, shi kuma ya kebanci muminai masoyansa da ita.

Allah ya girmama Manzon Allah (SAW) da abin da bai girmama wani dan Adam da shi ba. Ya daukaka ambatonsa, ta inda ya hada sunansa da sunan Annabi (SAW). Indai an kira sunan Allah, sai an kira sunan Annabinsa.

Allah ya yi masa budi (Fatahi) na Zahiri – Sulhu a Hudaibiyya, Fat’hu Khaibara, da Fat’hu Makkah; da Badini – Fatahi a Sifa, Fatahi a Suna da Fatahi a Zati.

Allah ya gafarta wa Manzon Allah (SAW), ya tafiyar da dauda ga ‘ya’yan gidansa, ya yi Isra’i da shi, ya rantse da zamaninsa da garin da aka haife shi, ya ba shi alkairi mai yawa (Alkausar), sannan kuma mu’ujizarsa ta wanzu har tashin alkiyama. Zamaninsa yana kara tsawo mu’ujizarsa tana kara fitowa amma sauran Annabawa, akasin haka ne.

Allah ya aiko Manzon Allah (SAW) zuwa ga halitta baki daya, Annabin duka nahiyoyin duniya ne.

Ya zo a cikin maganar waliyyai na abin da suka fada dangane da bambancin Annabi (SAW) a matsayin “Habibullahi” da Annabi Ibrahim AS a matsayin “Kalilullahi”: mukamin Annabi Ibrahim shi ne kwadayin gafara, saboda jirwaye mai kamar wanka da ya yi kan wata waki’a biyu da ta faru da shi; 1. Ya sare gumaka, ya ce a tambayi babbansu 2. Ya kira matarsa, Saratu da cewa ‘yar uwarsa ce.

Amma a bangaren Annabi (SAW), Ubangiji bai fadi laifin ba sai dai hukuncin kawai, da cewa, “mu muka yi maka budi, budi mabayyani, don mu yafe maka laifinka da wanda ka yi, da wanda za ka yi gaba…”, Abun nufi a nan, ittifakan Allah ya gafarta wa Annabi Ibrahim (AS) amma gafarar da aka yi wa Annabi (SAW), sai da aka hado ta da Gara – budi bayyananne, da gafarar abin da ya gabata da wanda zai zo a nan gaba, cika ni’imarsa a kan Habibinsa, shiriya kan tafarki madaidaici, da taimakon nasara mabuwayiya. Babu yadda za a yi wanda ke neman gafara ya yi daidai da wanda aka hado shi da irin wannan Gara.

Annabi Ibrahim ya roki Allah kar ya tozartar da shi ranar Alkiyama, amma shi Annabi (SAW), Ubangiji bai bayyana inda ya roka ba duk da cewa yana roko, sai ga shi Ubangiji ya sanya wa ranar Alkiyama suna da “ranar da Allah ba zai tozartar da Annabi (SAW) da wadanda suka yi imani da shi ba.” Alhamdulillah… duk wanda ya yi imani da Annabi (SAW), ya tsira. Duk wannan ukuba da ake ruwaitowa ta ranar Alkiyama, ba wanda yace karya ne amma wanda ya amsa Darikar Shehu Tijjani (Abul Abbas), sai dai ya farka a Aljannah ya ji duk an gama komai, wata kila aka ce Shehu ina hujjar fadin wannan, sai ya ce, Hadisi ya zo, ranar Alkiyama Umar zai amsa littafinsa na Shari’a da hannun dama, sai aka ce, ina Abubakar fa, aka ce yana cikin Aljannah lokacin.

Annabi Ibrahim (AS) ya roki Allah ya sa a yi ta yabonsa, ana fadin aikin alkairinsa har tashin Alkiyama, kuma Allah ya amsa masa wannan. Duk addinatai suna iya fadan batanci a kan wasu Annabawa amma Annabi Ibrahim duk addinatai suna yabonsa, kowa cewa yake nashi ne, sabida wannan addu’a (waj alliy lisana sidkin fil akhirin). Amma Annabi (SAW), ba a fada inda ya roka ba, sai ga shi Ubangiji yana ce masa (wa rafa’ana laka zikraka) mu muka daukaka ambatonka. Annabi (SAW) ya ce, ya Jibrilu mece ce fassarar haka? Ya ce, ban sani ba amma bari in tambaya, Jibrilu ya dawo da amsar cewa, Ubangijinka na nufin, duk in an ambace shi, sai an ambace ka. To yanzu ne aka yi zikiri. Ina masu da’awar Akida? Masu shirin sai sun kawar da ambaton Annabi (SAW), to Sahabbai dai sun gane! A yayin da ake yakin zubar da jini, ana sare wuya amma Annabi suke kira (ya Muhammada) kuma ba su yi shirka ba. A ko ina aka ambaci Ubangiji sai an ambaci Annabinsa (SAW). A wasu wurare ma da yawa a Alkur’ani Allah ya hade sunansa da Annabinsa (SAW), “wallahu wa rasuluhu a hakku an yurduhu – da Allah da Annabinsa, shi yafi cancanta a yarda da shi”.

Annabi Ibrahim ya yi addu’ar cewa, Ubangiji ya tsare shi da zuriyarsa daga bautar gunki, wanda ake bautama wa, amma ‘yar tsana, ko zanen sarakuna ko na mazan jiya da ake zanawa don jinjina ba don bauta ba, wannan ba sunan shi gunki ba. Annabi Ibrahim yana nufin zuriyarsa ta bar bautar Ubangiji ta koma ta Gumaka, Allah ya tsare su. Kuma Allah ya yi masa haka.

Da wannan, wasu Malamai suka kafa hujjar cewa, iyayen Annabi (SAW), suna kan addinin Annabi Ibrahim (Hanafi).

Annabi Ibrahim ya roki Ubangiji ya tsare shi da zuriyarsa daga bautar gunki amma Annabi (SAW), Allah ne ya tafiyar da kazanta daga zuriyarsa da ke cikin bargo gaba daya ba bautar gunki kadai bai.

Mece ce kazanta (Rijsu)? Giya da caca da bautar gumaka, da kuma rantsuwa da gumaka. Sannan kuma, ya tsarkake su tsarkakewa. Don haka, yadda dan Adam ba zai iya tashi sama ba, haka zuriyar Annabi (SAW) ba za ta iya sabo ba. Da wannan za mu fada cewa, Annabi Ibrahim ya roki abu daya, amma Annabi (SAW) sai da aka bashi hudu.

 

Fadakarwa game da cikar Manzon Allah (SAW) shekara 1,500 da haihuwa

Muna kira ga daukacin al’ummar Musulmi kowa ya yi tanadi na musamman kar ya bari a bar shi a baya, Allah ya kawo mu watan Rabi’ul Auwal, maulidin da za a yi na ranar 12 ga watan shi ne zai zama Manzon Allah (SAW) ya cika shekaru 1,500 da haihuwa.

Yadda abin yake shi ne, idan ka dauki shekarun haihuwar Manzon Allah (SAW) 40 kafin a fara aiko masa da manzanci ka hada da shekarun da ya yi a Makkah guda 13 bayan fara saukar da manzanci, zai ba ka shekaru 53. To, idan ka hada shekaru 53 da shekarar Hijira 1447 ta bana, lissafin zai ba ka cewa Manzon Allah (SAW) ya cika shekaru 1500 da haihuwa.

Hatta wadanda ba su yin maulidi ya kamata a bana su yi kokari su yi wani abu ko yaya kar a bar su a baya, saboda yanzu da Allah ya ja da rayuwarmu muka ga watan Rabi’ul Auwal na bana, lokacin da Manzon Allah ya cika shekara 1,500 da haihuwa, to zai yi wahala mu ga lokacin da zai cika shekara 2,000 kuma. Domin da wahala a samu wani daga cikin mutanen da ke rayuwa a doron kasa yanzu da zai kara wasu shekaru 500 a raye.

A lokacin da Annabi Isah (AS) ya cika shekaru 2,000 da haihuwa an ga yadda duk duniya ta dauki murna, to mu ma ya kamata Musulmi mu girgiza duniya da bukukuwa na murnar mu ma Annabinmu (SAW) ya cika shekaru 1,500 a duniya. Wannan babban alheri ne da tarihi a rayuwarmu. Allah ya hore mana dukkan abun da za mu yi hidima da shi Albarkar Annabi (SAW).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)
Dausayin Musulunci

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi
Dausayin Musulunci

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

October 3, 2025
Next Post
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta'addanci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.