ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
11 months ago
Ta'addanci

Sa’oi 24 da Fadar Shugaban kasa ta bigi ikirarin cewa, ofishin Malam Nuhu Ribadu a watanni 24 da suka gaba, ya samu nasara kan yakin da ke yi da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindigan Daji, kwatsam, sai kuma a makwannin da suka wuce, wasu mahara suka kutsa cikin wani Masallaci a garin Malumfashi na jihar Katsina suka kai mummunan hari a yayin da masallatan ke kan tsakiya da gabatar da Sallar Asuba, suka hallaka masallata 30.

 

Sai dai, abin da ake cewa wai, ihu bayan hari, daga baya jami’an tsaro a garin sun nemi daukin sauran jami’an tsaro domin kai dduki bayan maharan sun kaddamar da harin na su.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?
  • Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Fadar Gwamnatin kasa ta yi ikirarin cewa, Gwamnatin kasar ta gaji matsalar tsaron ne, daga Gwamnatin baya, amma ta yi ikirarin cewa, bisa dabarun da Nuhu ya samar, musamman ta hanyar yi wa tsarin tsaron kasar garambawul, da kuma yin aikin hadaka da sauran hukumomin tsaro, hakan ya sanya ofishin na Nuhu, samun nasara a wanzar da ayyukan tsaro na sirri, tare da kuma yin hadaka da hukumomin tsaro na kasa da kasa, musamman domin a kara karfafa tsaro a cikin kasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Ba wai muna yin jayya da sanarar da ofishin Nuhu ya samu a tsakanin wadannan watanni ba ne kuma muna sane da kokarin da yake yi, na ganin cewa, ‘yan Nijeriya na samu su kwanta su yi barcin dare, idanuwansu biyu a rufe ba tare da wata fargabar ko za a kai masu hari ba.

 

Tabbas, muna jinjina masa kan yunkurin da yake ci gaba da yi na rage kalubalen rashin tsaro da Gwamnatin mai ci ta gada.

 

Amma mummunan harin da wasu mahara suka kai a watannin baya a yankin Yelwata, inda suka yi wa wasu al’umomin yankin kisan kiyashi da kuma harin da ‘yan bindiga suka kai kan Masallaci a garin Malumfashi ta Jihar Katsina, ba makawa hakan ya nuna cewa, kamar an yi gaggawa kan ga murnar samun nasara ta yakin da ofishin Nuhu ke kan yi, da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga Daji duk da kuwa nasarar kame da kuma kashe wasu kasurguman ‘yan ta’adda da ofishinsa ya yi.

 

Kazalika, irin wannan salon ikirarin samun nasara a yakin da ‘yan ta’adda ne, Gwamnatin da ta shude ta rinka shelanata cewa, ta samu, amma a zari, batun akwai lauje a cikin nadi.

 

Domin kuwa, kusan shekaru takwas na Gwamnatin da ta gabata ta yi, kalubalen rashin tsaro ya jefa rayuwarsu, a cikin tasku, duba da yadda ‘yan tayar da kayan baya a kasar suka kusan durkusar da bangaren tsaron kasar, ta hanyar aikata ayyukansu na ta’addacin wanda lamarin ya kai ga har an nuna bukatar a yi wa fannin tsaron garanbawul.

 

Bugu da kari, ‘yan Nijeriya da dama,, sun ta yin kiraye-kirayen da a dauki mataki kan kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar a zahirance, ba wai kawai yin bayanai, da fatar biki da hukumomin tsaron kasar ke yi na cewa, sun kurmushe kaifin ‘yan ta’addar Kungiyar Boko Haram.

 

Hakazalika, a tsakanin wadannan watannin, manyan hukumomin tsaro na kasa sun ta yin bayanan zaurance domin nunawa ‘yan kasa tamkar komai na tafiya daidai, bayan alhali a bayan fage, ‘yan ta’adda na ta kai komon, yunkurin durkusar da kasa.

 

Har zuwa yanzu, ‘yan Nijeriya na ci gaba da zama a cikin kwankwaton ikirarin da hukumomin tsaron kasar ke yi na murkushe kaifin ‘yan Boko Haram inda kuma a zahirance, ake ganin ‘yan gudun hijira a yankin Arewa Maso Gabas ke kara kwarara zuwa sansanonin ‘yan gudun hijira da ke a yankin domin tsira da rayuwarsu.

 

A gefe daya kuma, manyan hanyoyin kasar sun koma tamar tarkon mutuwa ga matafiya inda ake tare su, a wasu yankuna, a hall aka su.

 

Masu garkuwa da mutane da sauransu, na ci gaba hana ‘yan Nijeriya sakat saboda ayyukansu da suke ci gaba da gudanarwa.

 

An dai nada Nuhu Ribadu a mukamin mai bai wa shugaban kasa shawara ne, bisa la’akari da nasarorin da ya samar, a lokacin da ya kasance shi ne shugaba na farko, na hukumar EFCC.

Nuhu tsohon Dansanda ne, wanda ya yi ritaya, a matsayin mataikin Sifeta Janar na ‘Yan Sanda.

Amma idan har zamu yiwa hukumomin tsaron adalaci, za mu iya cewa sun yi kokar wajen kashe ‘yanbindiga da dakile hare-haren ‘yan ta’adda a jihohohi kamar Zamfara, Katsina, Kaduna da Sokoto.

Sai dai, bisa maganar gaskiya, har yanzu za a iya cewa, akwai sauran gagarumin jan aiki, a gaba, game da magance matsalolin rashin tsaro a kasa.

Kalubalen rashin tsaro da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da fuskanta matsala ce da ke bukatar yin tunani mai zurfi da bunkasa salon dabarun yaki tare da daukar kwararan matakan da suka kamata, domin a kawo karshenta.

Kamata ya a ce, ofishin Nuhu Ribadu ya zama tamkar cibiyar da za a zauna a wasa kwakwalwar yin nazarin tsara yadda za a tunkari kalubalen rashin tsaron musamman duba da cewa, zuwa kai farmaki fagen daga ba hurumin sa ba ne.

Malam Nuhu Ribadu na da bukatar samun kwararru da za su taimaka masa da kuma shi kan shi tsarin tsaron kasa.

Bugu da kari, batun na samun nasara a yakar ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga, ba shi ne abin da a yanzu ‘yan kasa ke bukatar ji ba, domin a namu ra’ayin abin da suke bukata daga gun hukumomin tsaron shi ne, kara jajircewarsu wajen samar da dawamamen zaman lafiya a kasa.

Muna kira ga Malam Nuhu Ribadu da ya yi amfani da karfin ofishinsa wajen kara matsawa dakarun soji da ke a fagen daga na su kara kwazo kan yakin da suke ci gaba da yi da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga.

A namu ra’ayin, nuna ganin kamar an yi riga Malam Masallaci kan batun cewa, an samu nasara kan yakar ‘yan tayar da kayar baya a kasar nan, musamman duba da cewa, har yanzu ‘yan Nijeriya na ci gaba da zama a cikin fargabar hare-haren’yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda.

Kazalika, duba da cewa, masallata a Masallatai na gudanar da ibada a cikin jimanin tsoro, wannan babban abin nuna damuwar ne bayan cewar, nauyi ne a kan jami’an tsaro su tabbatar da suna kare rayuka da dukokiyoyin ‘yan kasar .

Rashin imanin da ya aku a jihar Katsina da kuma a yankin Yelwata abune da ya nuna irin gazawar da ake da ita, bangaren samun bayanan sirri. A yayin da muke taya Fadar Shugaban kasa murnat samun wannan nasarar ,amma muna ganin har yanzu akwai sauran jan aiki a gaba kan batun kalubalen rashin tsaro a kasar.

Ta'addanci
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
Ta'addanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
  • Sulaiman
    Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Yadda Aka Gudanar Da Taron Ranar Hausa Ta Duniya A Masarautar Daura

Yadda Aka Gudanar Da Taron Ranar Hausa Ta Duniya A Masarautar Daura

LABARAI MASU NASABA

Ta'addanci

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.