ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
9 months ago
Ta'addanci

Sa’oi 24 da Fadar Shugaban kasa ta bigi ikirarin cewa, ofishin Malam Nuhu Ribadu a watanni 24 da suka gaba, ya samu nasara kan yakin da ke yi da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindigan Daji, kwatsam, sai kuma a makwannin da suka wuce, wasu mahara suka kutsa cikin wani Masallaci a garin Malumfashi na jihar Katsina suka kai mummunan hari a yayin da masallatan ke kan tsakiya da gabatar da Sallar Asuba, suka hallaka masallata 30.

 

Sai dai, abin da ake cewa wai, ihu bayan hari, daga baya jami’an tsaro a garin sun nemi daukin sauran jami’an tsaro domin kai dduki bayan maharan sun kaddamar da harin na su.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?
  • Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Fadar Gwamnatin kasa ta yi ikirarin cewa, Gwamnatin kasar ta gaji matsalar tsaron ne, daga Gwamnatin baya, amma ta yi ikirarin cewa, bisa dabarun da Nuhu ya samar, musamman ta hanyar yi wa tsarin tsaron kasar garambawul, da kuma yin aikin hadaka da sauran hukumomin tsaro, hakan ya sanya ofishin na Nuhu, samun nasara a wanzar da ayyukan tsaro na sirri, tare da kuma yin hadaka da hukumomin tsaro na kasa da kasa, musamman domin a kara karfafa tsaro a cikin kasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Ba wai muna yin jayya da sanarar da ofishin Nuhu ya samu a tsakanin wadannan watanni ba ne kuma muna sane da kokarin da yake yi, na ganin cewa, ‘yan Nijeriya na samu su kwanta su yi barcin dare, idanuwansu biyu a rufe ba tare da wata fargabar ko za a kai masu hari ba.

 

Tabbas, muna jinjina masa kan yunkurin da yake ci gaba da yi na rage kalubalen rashin tsaro da Gwamnatin mai ci ta gada.

 

Amma mummunan harin da wasu mahara suka kai a watannin baya a yankin Yelwata, inda suka yi wa wasu al’umomin yankin kisan kiyashi da kuma harin da ‘yan bindiga suka kai kan Masallaci a garin Malumfashi ta Jihar Katsina, ba makawa hakan ya nuna cewa, kamar an yi gaggawa kan ga murnar samun nasara ta yakin da ofishin Nuhu ke kan yi, da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga Daji duk da kuwa nasarar kame da kuma kashe wasu kasurguman ‘yan ta’adda da ofishinsa ya yi.

 

Kazalika, irin wannan salon ikirarin samun nasara a yakin da ‘yan ta’adda ne, Gwamnatin da ta shude ta rinka shelanata cewa, ta samu, amma a zari, batun akwai lauje a cikin nadi.

 

Domin kuwa, kusan shekaru takwas na Gwamnatin da ta gabata ta yi, kalubalen rashin tsaro ya jefa rayuwarsu, a cikin tasku, duba da yadda ‘yan tayar da kayan baya a kasar suka kusan durkusar da bangaren tsaron kasar, ta hanyar aikata ayyukansu na ta’addacin wanda lamarin ya kai ga har an nuna bukatar a yi wa fannin tsaron garanbawul.

 

Bugu da kari, ‘yan Nijeriya da dama,, sun ta yin kiraye-kirayen da a dauki mataki kan kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar a zahirance, ba wai kawai yin bayanai, da fatar biki da hukumomin tsaron kasar ke yi na cewa, sun kurmushe kaifin ‘yan ta’addar Kungiyar Boko Haram.

 

Hakazalika, a tsakanin wadannan watannin, manyan hukumomin tsaro na kasa sun ta yin bayanan zaurance domin nunawa ‘yan kasa tamkar komai na tafiya daidai, bayan alhali a bayan fage, ‘yan ta’adda na ta kai komon, yunkurin durkusar da kasa.

 

Har zuwa yanzu, ‘yan Nijeriya na ci gaba da zama a cikin kwankwaton ikirarin da hukumomin tsaron kasar ke yi na murkushe kaifin ‘yan Boko Haram inda kuma a zahirance, ake ganin ‘yan gudun hijira a yankin Arewa Maso Gabas ke kara kwarara zuwa sansanonin ‘yan gudun hijira da ke a yankin domin tsira da rayuwarsu.

 

A gefe daya kuma, manyan hanyoyin kasar sun koma tamar tarkon mutuwa ga matafiya inda ake tare su, a wasu yankuna, a hall aka su.

 

Masu garkuwa da mutane da sauransu, na ci gaba hana ‘yan Nijeriya sakat saboda ayyukansu da suke ci gaba da gudanarwa.

 

An dai nada Nuhu Ribadu a mukamin mai bai wa shugaban kasa shawara ne, bisa la’akari da nasarorin da ya samar, a lokacin da ya kasance shi ne shugaba na farko, na hukumar EFCC.

Nuhu tsohon Dansanda ne, wanda ya yi ritaya, a matsayin mataikin Sifeta Janar na ‘Yan Sanda.

Amma idan har zamu yiwa hukumomin tsaron adalaci, za mu iya cewa sun yi kokar wajen kashe ‘yanbindiga da dakile hare-haren ‘yan ta’adda a jihohohi kamar Zamfara, Katsina, Kaduna da Sokoto.

Sai dai, bisa maganar gaskiya, har yanzu za a iya cewa, akwai sauran gagarumin jan aiki, a gaba, game da magance matsalolin rashin tsaro a kasa.

Kalubalen rashin tsaro da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da fuskanta matsala ce da ke bukatar yin tunani mai zurfi da bunkasa salon dabarun yaki tare da daukar kwararan matakan da suka kamata, domin a kawo karshenta.

Kamata ya a ce, ofishin Nuhu Ribadu ya zama tamkar cibiyar da za a zauna a wasa kwakwalwar yin nazarin tsara yadda za a tunkari kalubalen rashin tsaron musamman duba da cewa, zuwa kai farmaki fagen daga ba hurumin sa ba ne.

Malam Nuhu Ribadu na da bukatar samun kwararru da za su taimaka masa da kuma shi kan shi tsarin tsaron kasa.

Bugu da kari, batun na samun nasara a yakar ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga, ba shi ne abin da a yanzu ‘yan kasa ke bukatar ji ba, domin a namu ra’ayin abin da suke bukata daga gun hukumomin tsaron shi ne, kara jajircewarsu wajen samar da dawamamen zaman lafiya a kasa.

Muna kira ga Malam Nuhu Ribadu da ya yi amfani da karfin ofishinsa wajen kara matsawa dakarun soji da ke a fagen daga na su kara kwazo kan yakin da suke ci gaba da yi da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga.

A namu ra’ayin, nuna ganin kamar an yi riga Malam Masallaci kan batun cewa, an samu nasara kan yakar ‘yan tayar da kayar baya a kasar nan, musamman duba da cewa, har yanzu ‘yan Nijeriya na ci gaba da zama a cikin fargabar hare-haren’yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda.

Kazalika, duba da cewa, masallata a Masallatai na gudanar da ibada a cikin jimanin tsoro, wannan babban abin nuna damuwar ne bayan cewar, nauyi ne a kan jami’an tsaro su tabbatar da suna kare rayuka da dukokiyoyin ‘yan kasar .

Rashin imanin da ya aku a jihar Katsina da kuma a yankin Yelwata abune da ya nuna irin gazawar da ake da ita, bangaren samun bayanan sirri. A yayin da muke taya Fadar Shugaban kasa murnat samun wannan nasarar ,amma muna ganin har yanzu akwai sauran jan aiki a gaba kan batun kalubalen rashin tsaro a kasar.

Ta'addanci
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
Ta'addanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Yadda Aka Gudanar Da Taron Ranar Hausa Ta Duniya A Masarautar Daura

Yadda Aka Gudanar Da Taron Ranar Hausa Ta Duniya A Masarautar Daura

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.