• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce duk da yake tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar ƙalubale, kwatanta shi kafaɗa-da-kafaɗa da na Venezuela da gwamnonin jam’iyyar PDP su ka yi rashin adalci ne.

Ya ce: “Mu na bayyana cewa, duk da yake ƙasarmu na fuskantar wasu matsaloli, waɗanda kuma wannan gwamnati ta Shugaba Tinubu na ƙoƙarin magancesu, amma matsalolinmu ko kusa ba su kai irin na kasar Venezuela ba, kamar yadda gwamnonin PDP su ka yi zargi.”

  • Adadin Zirga-zirgar Fasinjoji A Jiragen Kasa Ya Zarce Miliyan 230 A Rabin Farko Na Wa’adin Hutun Bikin Bazara
  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, ministan ya ce: “Tattalin arzikin Nijeriya har yanzu ya na da ƙarfi sosai, kuma ana sa rai da kyakkyawan hasashen cewa zai bunƙasa da ƙarin kashi 3 cikin 100 cikin wannan shekarar.

“Tattalin arzikin mu na bayar da gudunmawar lamuni ga masu rance a cikin gida da waje.”

A ranar Litinin ne Gwamnonin PDP su ka gudanar da taro a Abuja, inda suka tattauna batutuwa, musamman waɗanda su ka shafi matsalar tsaro da matsalar tattalin arziki, wacce ta haifar da tsadar rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

Bayan kammala taron, sun bada sanarwar cewa, sun amince kowace jiha a ba ta damar kafa ‘yansandan jiharta, domin shawo kan ƙalubalen matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan.

Amma a martaninsa, Ministan ya ce, “Mu na maraba da shawarwarin da su ka bayar waɗanda ba na son rai ba, domin ganin an magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki.

“A matsayinsu na shugabanni a gwamnatocin jihohi, gwammonin PDP su na da ‘yancin bayyana matsayarsu kan duk wani abu da ya shafi ƙasar nan.

“A matsayin gwamnonin PDP, waɗanda ya kamata a ce masu shiga sahun gaba ne kan inganta tattalin arziki, samar da yalwa a ƙasa da al’ummar jihohinsu, a ce kuma sun koma su na furta kalaman ƙage da shaci-faɗi kan Nijeriya, har su na kwatanta matsalar tattalin arzikin Nijeriya da irin matsalolin da su ka dabaibaye tattalin arzikin Venezuela.

“Mu na son mu bayyana cewa duk da yake dai tattalin arzikinmu na fuskantar ƙalubale, amma ko kusa ba daidai ba ne a kwatanta matsalar Venezuela da ta Nijeriya.

“Yayin da Gwamnatin tarayya ke biyan albashi da sauran haƙƙoƙin ma’aikata kan kari, kuma harkokin gwamnati na tafiya daidai-wa-daida, ya kamata ‘yan Nijeriya su tambayi gwamnonin PDP abin da su ka yi da kuɗaɗen da ake ba su.

“Saboda akwai rahoton bincike mai nuna cewa, yawancin jihohin PDP sun kasa biyan ‘yan fansho kuɗaɗensu na tsawon watanni da dama, haka albashin ma’aikata ma wasu ba su biya yadda ya kamata.

“Gwamnonin PDP na ƙin biyan garatutin ma’aikatan da su ka yi ritaya.

“Haka kuma wasu gwamnonin PDP ɗin har yau sun kasa biyan naira 30,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, shekaru huɗu da Gwamnatin Tarayya ta fara amfani da tsarin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Matsayin gwamnonin PDP kan tattalin arzikin NijeriyaMinistan Yaɗa LabaraiSabon shirin Gwamnatin Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

Next Post

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Related

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

5 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

7 hours ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

9 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

10 hours ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

12 hours ago
Next Post
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Tinubu

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.