• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce duk da yake tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar ƙalubale, kwatanta shi kafaɗa-da-kafaɗa da na Venezuela da gwamnonin jam’iyyar PDP su ka yi rashin adalci ne.

Ya ce: “Mu na bayyana cewa, duk da yake ƙasarmu na fuskantar wasu matsaloli, waɗanda kuma wannan gwamnati ta Shugaba Tinubu na ƙoƙarin magancesu, amma matsalolinmu ko kusa ba su kai irin na kasar Venezuela ba, kamar yadda gwamnonin PDP su ka yi zargi.”

  • Adadin Zirga-zirgar Fasinjoji A Jiragen Kasa Ya Zarce Miliyan 230 A Rabin Farko Na Wa’adin Hutun Bikin Bazara
  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, ministan ya ce: “Tattalin arzikin Nijeriya har yanzu ya na da ƙarfi sosai, kuma ana sa rai da kyakkyawan hasashen cewa zai bunƙasa da ƙarin kashi 3 cikin 100 cikin wannan shekarar.

“Tattalin arzikin mu na bayar da gudunmawar lamuni ga masu rance a cikin gida da waje.”

A ranar Litinin ne Gwamnonin PDP su ka gudanar da taro a Abuja, inda suka tattauna batutuwa, musamman waɗanda su ka shafi matsalar tsaro da matsalar tattalin arziki, wacce ta haifar da tsadar rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Bayan kammala taron, sun bada sanarwar cewa, sun amince kowace jiha a ba ta damar kafa ‘yansandan jiharta, domin shawo kan ƙalubalen matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan.

Amma a martaninsa, Ministan ya ce, “Mu na maraba da shawarwarin da su ka bayar waɗanda ba na son rai ba, domin ganin an magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki.

“A matsayinsu na shugabanni a gwamnatocin jihohi, gwammonin PDP su na da ‘yancin bayyana matsayarsu kan duk wani abu da ya shafi ƙasar nan.

“A matsayin gwamnonin PDP, waɗanda ya kamata a ce masu shiga sahun gaba ne kan inganta tattalin arziki, samar da yalwa a ƙasa da al’ummar jihohinsu, a ce kuma sun koma su na furta kalaman ƙage da shaci-faɗi kan Nijeriya, har su na kwatanta matsalar tattalin arzikin Nijeriya da irin matsalolin da su ka dabaibaye tattalin arzikin Venezuela.

“Mu na son mu bayyana cewa duk da yake dai tattalin arzikinmu na fuskantar ƙalubale, amma ko kusa ba daidai ba ne a kwatanta matsalar Venezuela da ta Nijeriya.

“Yayin da Gwamnatin tarayya ke biyan albashi da sauran haƙƙoƙin ma’aikata kan kari, kuma harkokin gwamnati na tafiya daidai-wa-daida, ya kamata ‘yan Nijeriya su tambayi gwamnonin PDP abin da su ka yi da kuɗaɗen da ake ba su.

“Saboda akwai rahoton bincike mai nuna cewa, yawancin jihohin PDP sun kasa biyan ‘yan fansho kuɗaɗensu na tsawon watanni da dama, haka albashin ma’aikata ma wasu ba su biya yadda ya kamata.

“Gwamnonin PDP na ƙin biyan garatutin ma’aikatan da su ka yi ritaya.

“Haka kuma wasu gwamnonin PDP ɗin har yau sun kasa biyan naira 30,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, shekaru huɗu da Gwamnatin Tarayya ta fara amfani da tsarin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Matsayin gwamnonin PDP kan tattalin arzikin NijeriyaMinistan Yaɗa LabaraiSabon shirin Gwamnatin Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

Next Post

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Related

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

45 minutes ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

2 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

10 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

11 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

13 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

15 hours ago
Next Post
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

LABARAI MASU NASABA

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.