• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marwa Ya Sadaukar Da Karramawar LEADERSHIP Ga Buhari Da Jami’an NDLEA

Lambar Yabon Za Ta Taimaka Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Marwa Ya Sadaukar Da Karramawar LEADERSHIP Ga Buhari Da Jami’an NDLEA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya (NDLEA), Birgediya Janal Buba Marwa (mai ritaya), ya gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari da illahirin ma’aikatansa kan nasarar lashe lambar yabon jaridar LEADERSHIP ta garzon shekarar 2022 da ya samu.

Marwa ya ce, in ba don goyon bayan shugaban kasa da jami’an NDLEA ba, wadanda suke shiga kwararo-kwararo domin gudanar da ayyukan hukumar ba, shi din ba zai kai ga irin nasarorin da ya samu cimmawa a hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyin.

  • TARON LEADERSHIP: Buhari Ya Sauya Fasalin Tsarin Tattalin Arzikin Nijeriya —Ministan Abuja

Kan lambar yabon, Marwa ya ce, tabbas hakan zai kara masa kumaji da karsashin zage damtse wajen yaki da fataucin miyagun kwayoyi da dangoginsu a fadin kasar nan.

Da ya ke magana gefen wajen babban taron kamfanin rukunin jaridun LEADERSHIP da bikin mika lambar yabo ga gwaraza da ya gudana a ranar Talata, Marwa ya kara da cewa, “Dole mu gode wa shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa dukkanin goyo bayan da yake ba mu da kuma karfafarsa wajen ganin mun gudanar da ayyukanmu yadda ya kamata.

“Kuma dole ne mu jinjina tare da yaba wa jami’an hukumarmu, wandada su ne sojan kafa da suke gudanar da ayyukanmu yadda ya kamata. Ina jinjina ga jami’anmu maza da mata, ba don su din ba, da ban zo nan wajen a matsayin gwarzo ba.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

“Wannan lambar yabon za ta kara mana himma, za ta taimaka mana wajen cigaba da yakin da muke yi. A yakin da muke yi muna samun nasarori kuma za mu cigaba da samun nasara.”

Babban taron kamfanin rukinin jaridar LEADERSHIP mai wallafa jaridun Leadership, Leadership Hausa, National Economy da sauransu na 2022 mai taken “Sahihin Zabe Da Tattalin Arziki A Fagen Sauyi”, mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ne ya jagoranta, ya yin da tsohon Firaministan Kenya, Raila Odinga ya kasance babban bako mai gabatar da jawabi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sarkin Dutse, Dakta Nuhu Sunusi

Next Post

Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

7 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

9 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

10 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

11 hours ago
Next Post
Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato

Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.