ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato

by Sadiq
4 years ago
Tambuwal

Mataimakiya ta musamman ga Gwamna Aminu Waziri Tambuwal kan harkokin Ilimin mata, Hajiya Aishat Maina ta rasu.

Ta rasu ne bayan halartar taron gangamin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP da ya gudana a Jihar Sakkwato a ranar Talata.

  • Sin Na Tsayawa Tsayin Daka Kan Yaki Da Ta’addanci
  • Da Dumi-Dumi: Mahara Sun Kashe DPO Da Wasu A Benue

Leadership Hausa ta gano cewa, ta shiga cikin turmutsitsin da ya afku a kofar fitta daga filin taron.

ADVERTISEMENT

“Wani direban babur ne ya fado daga kan babur dinsa a hanyar fita dava filin wanda hakan ya haifar da mumunan turmutsutsu, inda mutane suka fado kan juna. Tana daya daga cikin wadanda abin ya shafa,” cewar wata majiya.

Da yake tabbatar da hakan, shugaban kungiyar masu ba da shawara na musamman, Ibrahim Magaji Gusau, ya ce an ceto marigayiyar, inda aka garzaya da ita Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato domin yi mata magani.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Abun takaici ta mutu ‘yan mintuna kadan bayan kai ta asibiti,” in ji shi Magaji, wanda ya bayyana ta a matsayin mai kwazo da hazaka.

“Ko a lokacin taron, muna tare, ba tare da sanin cewa hakan zai zama taronmu na karshe ba,” in ji shi, ya yi mata addu’ar Allah ya gafarta mata kurakuranta, ya kuma sanya ta a Jannatul Firdaus.

Marigayiyar dai tsohuwar shugabar kungiyar ‘yan jarida ce ta kasa (NAWOJ) a Jihar Sakkwato.

Ta kuma kasance tsohuwar mai bai wa Gwamna Aminu Tambuwal shawara kan sabbin kafafen yada labarai kafin a dauke ta zuwa Hukumar Ilimi ta Mata.

Tsohon Shugaban Kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) a Jihar Sakkwato, Isa Abubakar Shuni, ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar ‘yar jaridar ba zato ba tsammani, inda ya bayyana cewa ta ba da gudunmawa sosai ga harkar aikin jarida a jihar.

Ta rasu ta bar ‘ya’ya uku da kuma iyayenta tsofaffi.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya – Atiku 

Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya - Atiku 

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.