• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

by Sani Anwar
2 hours ago
in Rahotonni
0
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen hula (CSOs) da manyan masana kimiyyar siyasa, sun bayyana damuwarsu cewa; matukar ba a magance matsalar rashin daidaito da akida wajen aiwatar da manufofin jam’iyyuba, babu shakka; ba za a iya samun ingantaccen shugabanci ba, musamman a jihohi.

Yayin zantawa da LEADERSHIP, sun zargi gazawar tsarin jam’iyyun siyasa a halin yanzu.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

Har ila yau, sun tuna da cewa; kowace jam’iyyar siyasa a jamhuriya ta biyu, tana da akida guda daya da kuma bayyanannen tsari, wanda gwamnatin jam’iyyar ta aiwatar a kowane mataki.

Sannan sun lura cewa, jam’iyyun siyasa a halin yanzu; ba su da akidar siyasa, kuma mambobinta ba su da da’a wajen aiwatar da tsarin nasu, hatta a jihohin da suke mulki.

Kazalika, sun koka kan yadda shugabannin kasa da gwamnoni suka kwace jam’iyyu, tun bayan komawar mulkin demokuradiyya a shekarar 1999, manazartan sun yi nuni da cewa; alkawuran da aka yi wa al’umma a lokacin yakin neman zabe, yanzu ya koma na jam’iyya.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

Yayin da aka ce jam’iyyun siyasa a jamhuriya ta farko, sun fi karkata kan yanki, an yi yunkurin kafa jam’iyyun kasa a jamhuriya ta biyu da gangan.

A wancan jamhuriyar (1979–1983), manyan jam’iyyun siyasar Nijeriya su ne GNPP, NPN, NAP,NPP, PRP, da kuma UPN.

Duk da cewa, jam’iyyun sun banbanta a akida; amma ana ganin jam’iyyun UPN da PRP, a matsayin na masu fafutuka da kuma jajircewa, domin kuwa jam’iyyar UPN ta tsaya tsayin-daka wajen aiwatar da manufofinta.

An gina tsarin jam’iyyar bisa manyan manufofi hudu kamar haka: ilimi kyauta tun daga makarantar reno har zuwa manyan makarantu, harkar kiwon lafiya kyauta, hadin gwiwar karkara da ci gabanta da kuma samar da cikakkun ayyukan yi masu dorewa. Wadannan alkawura, an bi su ne bisa tsari na addini a jihohin da suka yi mulki, wato Jihar Legas, Oyo, Ogun, Ondo, da kuma Bendel.

A halin da ake ciki yanzu, yunkurin daidaita daidaito wajen aiwatar da tsarin ya samu matsala, a cewar rahoton LEADERSHIP.

LEADERSHIP ta tuna cewa, yunkurin da gwamnonin jihohi suka yi a baya na aiwatar da tsarin duba takwarorinsu a karkashin kungiyar gwamnonin Nijeriya, yanzu abin bah aka yake ba.

Yayin da jam’iyyar APC mai mulki da kuma jam’iyyar adawa ta PDP ke ci gaba da gudanar da taron gwamnoninsu, an nuna damuwa kan rashin aiwatar da muhimman tsare-tsaren jam’iyyar da kuma ci gaba da shirye-shiryen jam’iyyar ta hanyar gwamnatocin jam’iyyar daya da suka gaje su, wanda hakan ke haifar da manufofin jam’iyyar.

Wannan lamari dai ya kara yin tsamari sakamakon ficewar gwamnoni daga jam’iyyunsu.

Tun daga 1999, jam’iyyu sun zama tamkar wasu motoci ne da ake yin amfani da su, domin cin zabe;

 

Ba Za Mu Sake Bari Haka Ta Faru Ba – ADC

Sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa; rikicin da ke tattare rashin aiwatar da tsarin jam’iyyya na bai-daya a jihohin da jam’iyya daya ke mulki, na nuna cewa wata babbar matsala ce.

Ya ce, tun daga farkon jamhuriya ta hudu, jam’iyyu suka zama masu matukar rauni a cikin al’umma tare da kasancewa a matsayin wani dandali na ‘yan siyasa na tsayawa takara.

“Saboda haka, ba kamar jam’iyyun jamhuriya ta biyu ba, wadanda suka ginu a kan akidu, manufofi da kuma tsare-tsare. Jam’iyyun a wancan jamhuriyar, sun kasance tamkar wasu motoci na musamman, domin gudanar da zabe; saboda haka, don ba su da karfi; ba za su iya dora ikonsu ko akidunsu a kan daidaikun ‘yan siyasa ba.

“Don haka, idan kuna da jihohi shida a karkashin jam’iyya, sannan kuma kowannensu ya fitar da nasa tsarin ba tare da an ga akida daga jam’iyyar ba, to sai a ga irin wannan rashin jituwa, rabuwar kai ko kuma rashin jituwar ta yi yawa.

Ya kara da cewa, a jamhuriya ta biyu mutane sun zabi jam’iyyu ne saboda abin da za su samu.

“Shi yasa mutane irin su marigayi Chinua Achebe, sun shiga jam’iyyar PRP, saboda imani da ya yi da akidu da kuma manufofinta.”

“Amma ida za a iya tunawa, shugaban jam’iyyar ADC na kasa Sanata Dabid Mark ya ce; muna gina wannan jam’iyya ne, wanda ba za ta bar duk wanda aka zaba a ADC ya yi abin da ya ga dama ba bayan samun mulki. Daga rana ta farko, za mu mika wa zababbu manufofin da ke kunshe da wannan jam’iyya,” in ji shi.

Ya ce, idan har jam’iyyu za su iya bunkasa tsarin tafiyar da harkoki da manufofinsu na al’umma, duk wanda ya samu mukami dole ne ya aiwatar da manufofin jam’iyya, kamar yadda aka gani a jamhuriya ta biyu a karkashin jam’iyyar UPN.

Ya yi nuni da cewa, babbar mafita ita ce karfafa jam’iyyun siyasa tare da tabbatar da cewa; ba za su bison zuciyar mutane ba.

 

Dalilin Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Kasa Aiwatar Da Manufa Iri Daya- IPAC

Majalisar bayar da shawara kan jam’iyyu (IPAC), ta bayar da haske kan dalilan da suka haifar da wannan gazawa ta demokuradiyya tare da samar da hanya mai bullewa.

A wata tattaunawa da LEADERSHIP, shugaban IPAC na kasa, Dakta Yusuf Mamman Dantalle ya bayyana cewa; manufofin jam’iyya, wadanda ke tattare da akidu da manufofin da ke tsakanin jam’iyyun siyasa da masu zabe, sun zama tamkar wadansu takardu da ake yin watsi da su bayan kammala zabe.

Duk da haka, shugaban na IPAC ya lura cewa; fassarar alkawuran da aka yi a sakamakon gudanar da mulki, ya zama mai matukar wahala; saboda dalilai da dama, ciki har da inganta yanayin zamantakewa da tattalin arziki, banbancin da ke tsakanin jihohi da kuma na kananan hukumomi.

 

Akwai Bukatar Sauya Fasalin Tsarin Cikin Gaggawa – CISLAC

Da yake zantawa da LEADERSHIP kan wannan batu, babban jami’in tsare-tsare a cibiyar CISLAC, Suleiman Gimba ya nuna cewa; demokuradiyyar Nijeriya na fama da matsananciyar matsala, rashin daidaito, musamman wajen aiwatar da manufofin jam’iyya.

Ya bayyana yadda a baya aka taba kafa tsarin mulkin siyasa a karkashin jam’iyyu irin su UPN, wanda a halin yanzu abubuwan ba haka ake gudanar da su ba.

“Gwamnonin da aka zaba a jam’iyya guda, suna bin wasu manufofi daban-daban, wasu jihohin sun tafi a bangaren samar da ababen more rayuwa, wasu sun tafi a kan wasu abubuwa da ban, wasu kuma ma babu ruwansu da akidar da jam’iyyar tasu ta kafu a kai,” in ji Gimba.

“Dalili kuwa shi ne, saboda a yau; jam’iyyun suna aiki ne tamkar wasu na’urorin lashe zabe fiye da gwamnati.”

Gimba ya dora alhakin hakan a kan wasu muhimman abubuwa guda uku: raunin tsarin jam’iyya na cikin gida, rashin tushen akida da kuma rashin tsarin samar da kudade ga jam’iyyun siyasa.

A cewar tasa, idan ba tare da tallafin jama’a ko samar da wata hanyar shigowar kudade mai dorewa ba, jam’iyyu za su ci gaba da yin garguwa da masu hannu da shuni da kuma masu rike da madafun iko ne, wadanda ke bankado ayyukansu.

Gimba ya kara kwatanta shugabannin Nijeriya da alakarsu da jam’iyyun siyasa.

Ya ce, Obasanjo ya nuna karfi tare da juya jam’iyyarsa yadda yake so a lokacin mulkinsa, inda su ma shugabannin da suka biyo bayansa ke ci gaba da kwatanta hakan.

Kazalika, ya kawo misali da ajandar Tinubu ta ‘Renewed Hope Agenda’, wanda ya bayyana shirin a matsayin nasa na kashin kansa, maimakon na tsarin jam’iyyar APC.

“Babu shakka, wannan sauyi ya ci gaba da raunana jam’iyyun siyasa, yanzu haka muna da shugabannin zartarwa da ke mulki ta hanyar ka’idojin kashin kansu tare da kawar da akidun jam’iyya baki-daya, in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Next Post

Hadin Tsumin Baure

Related

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

5 hours ago
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC
Rahotonni

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

19 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

1 week ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 weeks ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

3 weeks ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

3 weeks ago
Next Post
Hadin Tsumin Baure

Hadin Tsumin Baure

LABARAI MASU NASABA

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Hadin Tsumin Baure

Hadin Tsumin Baure

September 27, 2025
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

September 27, 2025
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

September 27, 2025
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

September 27, 2025
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

September 27, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

September 27, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.