• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
5 months ago
in Nishadi
0
Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin wadanda aka assasa babbar masana’antar nishadi da ke amfani da harshen Hausa wajen isar da sako a fadin Duniya wadda ake wa lakabi da Kannywood kuma ta ke da matsugini a babban birni mai tarihi wato Kano,Tahir Fagge ya ce masana’antar a yanzu ta sauka daga kan turbar da tun farko aka gina ta akai.

Jarumin a wata hira da ya yi ya ce tun farko an gina masana’antar a kan wasu manyan tubali da suka hada da kaunar juna, shawarwari da kuma shugabanci nagari, amma yanzu an rasa wasu daga cikinsu saboda zuwan zamani da sauran dalilai.

  • Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya
  • Matsalar Tsaro: Matawalle Ya Ziyarci Jihar Zamfara

Tahir ya ce a baya duk wani dan Kannywood ya na matukar ganin dan uwansa ya samu karuwa idan kuma wata matsala ta faru dashi, zai jajanta mashi sannan idan akwai wani taimako da zai iya yi wajen fitar wannan damuwar zai yi ba kamar yanzu da kowa kanshi ya sani ba.

A zamanin baya idan wani zai shirya fim zai kawo labarin fim din a gaban manya a cikin masana’antar sai a duba a gani idan akwai wani gyara a yi idan kuma babu gyara sai a bashi shawarwarin da suka dace, sannan a baya akwai zumunci mai karfi a tsakanin wadanda ke cikin masana’antar, amma zuwan wayoyin hannu ya sa sai dai mutum ya kiraka a waya ya yi maka murna ko ya jajanta maka ba tare da ya zo har inda kake ba inji shi.

Dangane da shigowar manhajar YouTube da sauran shafukan yanar gizo inda ake dora fina finai a maimakon faifan cd da ake yi lokacin baya, Fagge ya kira wannan abu da ci gaban mai hakar rijiya domin kuwa ya na yin kasa ya na cewa an samu ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Idan kuka lura a baya mutum ya kan cire kudmdi kalilan ya yi fim dinsa mai kyau ya tafi kasuwa ya sayar ya samu riba mai yawa ba tare da wata tangarda ba, amma yanzu sai ka zuba makudan kudade wajen neman mabiya a shafukan yanar gizo wadanda za su dinga kallon fina finanka da kake dorawa lokaci bayan lokaci sannan ne za ka samu wani abin kirki.

Da aka tabo batun yadda wani lokaci a baya aka gane shi a wani waje wanda ake kyautata zaton gidan rawa ne kokuma gidan solo kamar yadda wasu suka sani, kuma har ta kai ga wadansu na ganin bai dace babban mutum kamar shi ya tafi irin wadannan wuraren da aka sani mafi yawancin wadanda ke wajen matasa ne da suka tafi domin a nishadantar dasu ba.

Tahir Fagge ya ce zuwa gidan solon da aka gani ya je ba haka kawai ya tafi ba, domin kuwa an iske shi har gida aka nemi ya tafi a matsayin babban bako a wurin wanda a wancan lokacin yake sabon budewa, bayan ya tafi ne kuma suka bukaci ya nishadantar da wadanda ke wajen kuma a matsayinsa na jarumi kuma wanda yake da masoya sai ya ga idan yaki ba za su ji dadi ba.

Bayan an saka wata wakar da a wajen aka rasa wanda zai iya taka rawar ta, duba da cewa tsohuwar waka ce sai ya yi zumbur ya tashi ya taka rawa domin ya nunawa matasan da ke wajen cewa da tsohuwar zuma ake magani, hakan ya sa mahukuntan wajen su ka ji dadi har suka yi mashi kyautar manyan kudade wanda a wannan lokacin yake da matukar bukatar kudi domin tafiya neman magani in ji shi.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Me Ke Kawo Yawan Tashin Gobara A Wannan Lokaci Na Hunturu?

Next Post

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

2 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 week ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.