• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
8 months ago
in Nishadi
0
Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin wadanda aka assasa babbar masana’antar nishadi da ke amfani da harshen Hausa wajen isar da sako a fadin Duniya wadda ake wa lakabi da Kannywood kuma ta ke da matsugini a babban birni mai tarihi wato Kano,Tahir Fagge ya ce masana’antar a yanzu ta sauka daga kan turbar da tun farko aka gina ta akai.

Jarumin a wata hira da ya yi ya ce tun farko an gina masana’antar a kan wasu manyan tubali da suka hada da kaunar juna, shawarwari da kuma shugabanci nagari, amma yanzu an rasa wasu daga cikinsu saboda zuwan zamani da sauran dalilai.

  • Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya
  • Matsalar Tsaro: Matawalle Ya Ziyarci Jihar Zamfara

Tahir ya ce a baya duk wani dan Kannywood ya na matukar ganin dan uwansa ya samu karuwa idan kuma wata matsala ta faru dashi, zai jajanta mashi sannan idan akwai wani taimako da zai iya yi wajen fitar wannan damuwar zai yi ba kamar yanzu da kowa kanshi ya sani ba.

A zamanin baya idan wani zai shirya fim zai kawo labarin fim din a gaban manya a cikin masana’antar sai a duba a gani idan akwai wani gyara a yi idan kuma babu gyara sai a bashi shawarwarin da suka dace, sannan a baya akwai zumunci mai karfi a tsakanin wadanda ke cikin masana’antar, amma zuwan wayoyin hannu ya sa sai dai mutum ya kiraka a waya ya yi maka murna ko ya jajanta maka ba tare da ya zo har inda kake ba inji shi.

Dangane da shigowar manhajar YouTube da sauran shafukan yanar gizo inda ake dora fina finai a maimakon faifan cd da ake yi lokacin baya, Fagge ya kira wannan abu da ci gaban mai hakar rijiya domin kuwa ya na yin kasa ya na cewa an samu ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Idan kuka lura a baya mutum ya kan cire kudmdi kalilan ya yi fim dinsa mai kyau ya tafi kasuwa ya sayar ya samu riba mai yawa ba tare da wata tangarda ba, amma yanzu sai ka zuba makudan kudade wajen neman mabiya a shafukan yanar gizo wadanda za su dinga kallon fina finanka da kake dorawa lokaci bayan lokaci sannan ne za ka samu wani abin kirki.

Da aka tabo batun yadda wani lokaci a baya aka gane shi a wani waje wanda ake kyautata zaton gidan rawa ne kokuma gidan solo kamar yadda wasu suka sani, kuma har ta kai ga wadansu na ganin bai dace babban mutum kamar shi ya tafi irin wadannan wuraren da aka sani mafi yawancin wadanda ke wajen matasa ne da suka tafi domin a nishadantar dasu ba.

Tahir Fagge ya ce zuwa gidan solon da aka gani ya je ba haka kawai ya tafi ba, domin kuwa an iske shi har gida aka nemi ya tafi a matsayin babban bako a wurin wanda a wancan lokacin yake sabon budewa, bayan ya tafi ne kuma suka bukaci ya nishadantar da wadanda ke wajen kuma a matsayinsa na jarumi kuma wanda yake da masoya sai ya ga idan yaki ba za su ji dadi ba.

Bayan an saka wata wakar da a wajen aka rasa wanda zai iya taka rawar ta, duba da cewa tsohuwar waka ce sai ya yi zumbur ya tashi ya taka rawa domin ya nunawa matasan da ke wajen cewa da tsohuwar zuma ake magani, hakan ya sa mahukuntan wajen su ka ji dadi har suka yi mashi kyautar manyan kudade wanda a wannan lokacin yake da matukar bukatar kudi domin tafiya neman magani in ji shi.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Me Ke Kawo Yawan Tashin Gobara A Wannan Lokaci Na Hunturu?

Next Post

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Related

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

4 days ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

4 days ago
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

2 weeks ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

4 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

1 month ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

1 month ago
Next Post
Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

LABARAI MASU NASABA

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.