ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
2 years ago
Tahir fagge

Daya daga cikin wadanda aka assasa babbar masana’antar nishadi da ke amfani da harshen Hausa wajen isar da sako a fadin Duniya wadda ake wa lakabi da Kannywood kuma ta ke da matsugini a babban birni mai tarihi wato Kano,Tahir Fagge ya ce masana’antar a yanzu ta sauka daga kan turbar da tun farko aka gina ta akai.

Jarumin a wata hira da ya yi ya ce tun farko an gina masana’antar a kan wasu manyan tubali da suka hada da kaunar juna, shawarwari da kuma shugabanci nagari, amma yanzu an rasa wasu daga cikinsu saboda zuwan zamani da sauran dalilai.

  • Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya
  • Matsalar Tsaro: Matawalle Ya Ziyarci Jihar Zamfara

Tahir ya ce a baya duk wani dan Kannywood ya na matukar ganin dan uwansa ya samu karuwa idan kuma wata matsala ta faru dashi, zai jajanta mashi sannan idan akwai wani taimako da zai iya yi wajen fitar wannan damuwar zai yi ba kamar yanzu da kowa kanshi ya sani ba.

ADVERTISEMENT

A zamanin baya idan wani zai shirya fim zai kawo labarin fim din a gaban manya a cikin masana’antar sai a duba a gani idan akwai wani gyara a yi idan kuma babu gyara sai a bashi shawarwarin da suka dace, sannan a baya akwai zumunci mai karfi a tsakanin wadanda ke cikin masana’antar, amma zuwan wayoyin hannu ya sa sai dai mutum ya kiraka a waya ya yi maka murna ko ya jajanta maka ba tare da ya zo har inda kake ba inji shi.

Dangane da shigowar manhajar YouTube da sauran shafukan yanar gizo inda ake dora fina finai a maimakon faifan cd da ake yi lokacin baya, Fagge ya kira wannan abu da ci gaban mai hakar rijiya domin kuwa ya na yin kasa ya na cewa an samu ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Idan kuka lura a baya mutum ya kan cire kudmdi kalilan ya yi fim dinsa mai kyau ya tafi kasuwa ya sayar ya samu riba mai yawa ba tare da wata tangarda ba, amma yanzu sai ka zuba makudan kudade wajen neman mabiya a shafukan yanar gizo wadanda za su dinga kallon fina finanka da kake dorawa lokaci bayan lokaci sannan ne za ka samu wani abin kirki.

Da aka tabo batun yadda wani lokaci a baya aka gane shi a wani waje wanda ake kyautata zaton gidan rawa ne kokuma gidan solo kamar yadda wasu suka sani, kuma har ta kai ga wadansu na ganin bai dace babban mutum kamar shi ya tafi irin wadannan wuraren da aka sani mafi yawancin wadanda ke wajen matasa ne da suka tafi domin a nishadantar dasu ba.

Tahir Fagge ya ce zuwa gidan solon da aka gani ya je ba haka kawai ya tafi ba, domin kuwa an iske shi har gida aka nemi ya tafi a matsayin babban bako a wurin wanda a wancan lokacin yake sabon budewa, bayan ya tafi ne kuma suka bukaci ya nishadantar da wadanda ke wajen kuma a matsayinsa na jarumi kuma wanda yake da masoya sai ya ga idan yaki ba za su ji dadi ba.

Bayan an saka wata wakar da a wajen aka rasa wanda zai iya taka rawar ta, duba da cewa tsohuwar waka ce sai ya yi zumbur ya tashi ya taka rawa domin ya nunawa matasan da ke wajen cewa da tsohuwar zuma ake magani, hakan ya sa mahukuntan wajen su ka ji dadi har suka yi mashi kyautar manyan kudade wanda a wannan lokacin yake da matukar bukatar kudi domin tafiya neman magani in ji shi.

 

Tahir fagge
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Ahanor Kan Fam Miliyan 40
Tahir fagge
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Tahir fagge
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.