Farfesa Filomene Ebi na jami’ar Alassane Ouattara na kasar Kwadifwa ya bayyana kasar Sin a matsayin mai tsare adalci a duniya, yana cewa martanin kasar kan karuwar aiwatar da ra’ayi na kashin kai da fafutukar neman iko a duniya, abu ne mai muhimmanci.
Filomene Ebi, farfesa a sashen nazarin dangantakar kasa da kasa a jami’ar wadda ke Abidjan, babban birnin harkokin tattalin arziki na kasar Kwadifwa ya kara da cewa, a matsayinta na mafi karfi a duniya, Amurka ta sanya karin harajin da ya shafi dukkannin kasashe, musammam masu tasowa, inda ya ce manufofin harajin na Amurka na yin mummunan tasiri kan galibin kasashen.
Ya ce a irin wannan yanayi, tsayuwar daka irin ta kasar Sin, za ta taimaka wajen tabbatar da daidaito kan batutuwan da suka shafi cinikayya da tabbatar da adalci.
Da yake bayyana muhimmancin tattaunawa da bin dokoki, Ebi ya ce duniya ta dogara ne kan tsarin dake daukaka tabbatar da dokoki a matsayin abun dake karfafa dangantakar cinikayya tsakanin kasa da kasa. (Mai Fassara: Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp