ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

by Sulaiman
1 year ago
Sanusi

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta sake jaddada haramta duk wani nau’in hawa a yayin bikin Sallar layya da ke gabatowa. Rundunar ta nanata haramcin ne sa’o’i kadan bayan Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi, ya umurci dukkan hakimai da ke karkashin masarautar Kano da su yi taro a birnin Kano domin gudanar da bikin na shekara-shekara.

 

LEADERSHIP ta rahoto cewa, a ranar Talata ne Majalisar Masarautar ta fitar da wata takarda inda ta umurci hakimai da dagatai da su zo da dawakansu da mahaya a ranar Laraba, 4 ga watan Yuni, a shirye-shiryen gudanar da bukukuwan hawan Sallah da ake sa rai. Majalisar ta kuma shirya wani taro a ranar Alhamis 5 ga watan Yuni a fadar mai martaba da ke Kofar Kudu domin zaman kammala shirye-shiryen gudanar da taron.

ADVERTISEMENT
  • FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22
  • Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Sai dai wata sanarwar manema labarai da rundunar ‘yansandan jihar Kano ta fitar, sa’o’i kadan bayan masarautar Kano ta sanar da tsare-tsarenta, ta sake nanata cewa, dokar hana duk wani nau’in hawan Sallah, wacce ta fara aiwatar da ita a lokacin bikin Sallar Azumi da ta gabata, tana nan kuma za ta ci gaba da wanzuwa har a lokacin bikin Sallar layya ta bana.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

“Saboda haka, rundunar ‘yansandan ta nanata cewa, dokar hana duk wani nau’in hawan Sallah a jihar yana nan, zai ci gaba da wanzuwa har zuwa lokacin bukukuwan Sallar Layya ta bana ta 2025 da ake shirin yi domin har yanzu, akwai barazanar tsaro mai karfi a jihar.

 

“An yanke wannan shawarar ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro biyo bayan rahotannin sirri da ke nuni da shirin wasu bata gari da masu daukar nauyinsu na yin amfani da bukukuwan hawan Sallah wajen gurgunta tsaro da zaman lafiya a jihar, kamar yadda aka tabbatar a lokacin Sallar Azumi.” In ji Rundunar

Sanusi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Sanusi
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.