• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Adamawa Ta Naɗa Hakimai 3 A Gundumar Ƙaramar Hukumar Hong

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

Masarautar Adamawa ta nada sababbin Hakimai a gundumomi uku na karamar hukumar Hong, biyo bayan dalilan mutuwa da tsofaffin hakiman yankin suka yi.

Zaben Hakiman wanda ya gudana a sakatariyar karamar hukumar Hong, gundumomin sun hada da Hildi da Uba da Gaya, da ke karamar hukumar ta Hong.

  • Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa
  • Gwamnatin Adamawa Ta Rantsar Da Sabbin Kantamomin Raya Karkara 50

An dai gudanar da zaben cike gurbin bisa gaskiya da adalci tare da sa’ido da kulawar Galadima Adamawa, Alhaji Mustapha Aminu, wanda ya wakilci Mai Martaba Lamido Adamawa, Alhaji Muhammadu Barkindo Aliyu Mustapha.

Sabbin Hakiman da su ka samu nasara a zaben sun hada da Abubakar Yusuf Hakimin Hildi, Suleiman Yahaya, Uba, da Adamu Suleiman Hakimin Gaya.

Da yake jawabi ga wadanda su ka samu nasarar zama sabbin Hakiman, Galadima Adamawa Mustapha Aminu, ya shawarce su da su kasance masu jajircewa, aminci da adalci wajen sauke nauyin da aka dora mu su.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Ya kuma tunatar da su manufofi da kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da zaman lafiya, ya ce su tabbata sun yi amfani da matsayin da su ka samu wajan taka muhimmiyar rawar tabbatarwa da samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummar da suke shugabanta.

Da shima ke jawabi a taron shugaban karamar hukumar Hong Usman Innuwa Wa’aganda, ya ta ya sabbin zababbun hakiman murna, ya yaba wadanda su ka sha kaye a zaben da yadda su ka rungumi kaddara, ya ce sun cancanci a yaba mu su.

A nasa jawabin, Amadadin sababbin Hakiman, Hakimin Hildi Abubakar Yusuf, ya godewa majalisar masarautu, gwamnatin jihar, da karamar hukumar Hong bisa wannan dama da aka ba su, ya kuma ba da tabbacin cewa za su rike Amana kamar yadda aka amince mu su.

Manyan baki da dama da su ka halarci taron sun hada da Wali Adamawa, Alhaji Aminu Abdulkadir, Wakili Alkalai, Mai shari’a Nathan Musa, Madawaki Adamawa, Usman Marafa, shugabannin bangarorin tsaro na karamar hukumar Hong.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adamawa
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

LABARAI MASU NASABA

Adamawa

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.