ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Zazzau Ya Buƙaci Addu’ar Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Sarkin Zazzau

Mai martaba Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga al’ummar Nijeriya da su ƙara duƙufa wajen gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali gami da yin addu’ar neman kawo ƙarshen matsalolin tsaro da suka addabi ƙasar nan.

Sarkin wanda ya yi wannan kiran a yayin bikin baje kolin al’adun gargajiya na shekara-shekara da Masarautar Kaltungo ta jihar Gombe ta saba shiryawa, ya kuma neman ƙarin addu’o’i wa gwamnatoci domin samun nasarar sauƙe nauyin da ke kawukansu wajen shawo kan matsalolin da ake fuskanta a ƙasar nan.

  • Tarihin Katsina Daga Karni Na Goma
  • Cire Tallafin Mai: Magani Mai Daci Ga Kashi 99 Cikin 100 Na ‘Yan Nijeriya

Nuhu Bamalli wanda shi ne uban taron, ya ce, babu wata ƙasa da za ta cigaba ba tare da zaman lafiya da kwanciyar hankali ba, don haka ne ya nemi jama’a da su kauce wa shiga dukkanin wani abun da ka iya janyo matsala ga zaman lafiyar ƙasa.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yaba wa Sarkin Kaltungo, Injiniya Sale Muhammadu Umar da ya kasance mai shirya taron da ke ƙara haɗa kan al’ummar masarautarsa da kuma yadda yake nuna damuwa wajen cigaban al’ummarsa haɗi da kiyaye tarihi da al’adun masarautar.

Sarkin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

Shi kuma a nasa jawabin, gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bada tabbacin gwamnatinsa na cigaba da kiyaye rayuka da dukiyar al’ummar jihar tare da bada gagarumin gudunmawa wajen bunqasa al’adun da jihar ke da su.

Gwamnan wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Dakta Manasseh Daniel Jatau, ya hori jama’a da a kowani lokaci su kasance masu mutunta sarakuna da al’adun gargajiya domin kyautata cigaba mai ɗaurewa.

Shi kuma a nasa ɓangaren, shugaban taro, Hon. James Joseph Damara (Kauran Kaltungo), ya gode wa irin shugabanci na kwarai da sarkin Kaltungon ke yi wajen kasancewa uba ga kowani ɗan masarautar haɗi da ‘yan uwanta da ke ƙara kyautata zaman lafiya a tsakanin al’ummar masmasarautar.

Ya ce, muhimmancin al’ada baya misaltuwa, yana mai cewa, a bisa mutunta al’ada ne manyan baƙi suka fito daga sassa daban-daban domin halartar wannan taron a Kaltungo, ya misalta sarkin garin a matsayin wani jarumin da ke da buƙarin haɗa kan jama’a da bunqasa al’adu da zaman lafiya a kowani lokaci.

A bikin dai wanda sarkin ya saba gudanarwa, ana baje kolin al’adun gargajiya da raye-raye gargajiya haɗi da baje nau’ikan kalolin abinci da ake da su a masarautar Kaltungo da ma makwafta, inda kowace ƙabila ke fitowa ta nuna asalin al’adarta da ke zama gwanin sha’awa ga mahalarta taro.

Taron wanda ake shafe kusan mako gudana a na gudanarwa, sarkin na kuma shirya taron liyafa na musamman wa ‘yan jarida da sarakuna da sauran manyan baƙi.

Sarkin Zazzau

A wajen liyafar da sarkin ya shirya wa ‘yan jarida, tsohon shugaban ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Bauchi, Malam Ibrahim Muhammad Malamgoje, ya yi kira ga masu hannu da shuni ko gwamnati da su kafa wata gidan rediyo ko talabijin a ƙaramar hukumar Kaltungo lura da yadda sarkin ke so da qaunar ‘yan jarida haɗi da mutunta aikin nasu.

A cewar Ibrahim wanda wakilin RFI Hausa ne, a dukkanin yankin arewa babu wani sarkin da ke gayyatar ‘yan jarida daga sassa daban-daban na ƙasar nan kawai domin ya zauna da su ya shirya musu ƙasaitaccen liyafa haɗi da jinjina wa irin qoqarin da suke bayarwa wajen cigaban ƙasa.

A nasa ɓangaren, Sarkin Kaltungo, ya ce, ‘yan jarida na da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen cigaban ƙasar nan, don haka akwai buƙatar a kasance ana jinjina wa irin ƙoƙarinsu a kowani lokaci. Kazalika ya kuma yaba wa irin ƙoƙarin jami’an tsaro su.

Ita kuma jigon taron, Hajiya Sa’adatu Saad Mustapha, ta ce, a kowani shekara ‘yan jarida sun kasance masu tallata irin al’adu da masarautar ke da su, don haka ne ta nuna ‘yan jarida a matsayin abokan jere.

Sarkin Zazzau
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Next Post
Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON – Peseiro

Zamu Dogara Da Osimhen Don Lashe Gasar AFCON - Peseiro

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.